ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

by Sadiq
53 minutes ago

Tsohon Gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, da Uwargidan Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, sun yi kira da a ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziƙin Shugaba Bola Tinubu bayan shekarar 2027.

Sun bayyana hakan ne ranar Alhamis a wani taron tsoffin shugabannin majalisun dokokin jihohi, wanda aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Lalong ya buƙaci ’yan Nijeriya su goyi bayan Tinubu domin ya sake zama shugaban ƙasa a karo na biyu, yana mai cewa gwamnati na buƙatar ƙarin lokaci domin kammala shirinta na sauye-sauyen tattalin arziƙi.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cire tallafin man fetur a matsayin mataki mai wahala wanda ya zama dole, yana mai cewa hakan zai bai wa gwamnati damar karkatar da kuɗaɗen da ake kashewa wajen tallafi zuwa fannoni kamar noma, masana’antu, ababen more rayuwa, ilimi, makamashi da fasaha.

Lalong ya ce Tinubu ya yi namijin ƙoƙari wajen ɗaukar matakan da gwamnatocin baya suka kasa ɗauka, yana mai cewa ya kamata a ba shi damar kammala ayyukan da ya fara.

LABARAI MASU NASABA

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

Ya kuma yi kira ga shugabannin siyasa da su riƙa bayyana wa ’yan Nujeriya dalilan da suka sa aka kawo sauye-sauyen, tare da tabbatar da cewa kuɗaɗen da aka samu sakamakon matakan ana amfani da su yadda ya kamata wajen bunƙasa tattalin arziƙi da samar da ayyukan yi.

A cewarsa, Nijeriya na buƙatar sauya tsarin dogaro da amfani da kayan gwamnati zuwa hanyoyin saka hannun jari.

Ita ma Uwargidan Shugaban Ƙasa ta yi kira da a kare nasarorin da gwamnatin ta samu domin amfanin ’yan Nijeriya na yanzu da kuma na nan gaba.

Ta yaba da goyon bayan da mahalarta taron suka nuna wa Tinubu domin ya sake tsayawa takara a karo na biyu, tana mai cewa hakan na da muhimmanci saboda ya fito daga tsoffin shugabannin majalisun jihohi da suka san ƙalubalen shugabanci da ɗaukar manyan matakan gwamnati.

Uwargidan Tinubu ta kuma buƙaci tsoffin ’yan majalisa da su ci gaba da bai wa ƙasa gudummawa, saboda ƙwarewarsu na iya taimakawa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya da koyar da matasa shugabanci.

An gudanar da taron ne ƙarƙashin taken “Jagoranci Na Gari, Sauye-Sauye: Daga Tallafi zuwa Sabon Muradi.”

MASU ALAKA

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa
Manyan Labarai

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

September 17, 2026
Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu
Labarai

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

September 17, 2026
An Ci TikTok Tarar Fam Miliyan £12.7 Kan Karya Dokar Kananan Yara A Burtaniya
Manyan Labarai

Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a

September 17, 2026
Next Post
Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23

September 17, 2026
Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

Lalong Da Uwargidan Shugaban Ƙasa Sun Goyi Bayan Ci Gaban Sauye-Sauyen Tinubu

September 17, 2026
Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK

September 17, 2026
 Xi Ya Yi Kira Da A Wanzar Da Kokarin Fadada Da Karfafa Ci Gaban Fannin Kere-kere

 Xi Ya Yi Kira Da A Wanzar Da Kokarin Fadada Da Karfafa Ci Gaban Fannin Kere-kere

September 17, 2026
2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

2027: Za Mu Kawo Wa Tinubu Kano Duk Da Tasirin Kwankwaso – Kofa

September 17, 2026
Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

Marafa Ya Yi Alƙawarin Murabus Idan Ya Kasa Magance Tsaro Cikin Shekaru Biyu

September 17, 2026
An Ci TikTok Tarar Fam Miliyan £12.7 Kan Karya Dokar Kananan Yara A Burtaniya

Hisbah Ta Cika Hannu Da Fitaccen Ɗan TikTok A Kano Kan Bidiyoyin Rashin Da’a

September 17, 2026
Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC

Tinubu Zai Shiga Tsakani A Rikicin Wike Da Gwamnonin APC

September 17, 2026
Kawayen amarya

’Yansanda Sun Ceto Mutane, Sun Daƙile Harin ’Yan Bindiga A Katsina

September 17, 2026
Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku

Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.