Iran ta sake musanta zargin cewa tana da wani ɓoyayyen wurin gudanar da ayyukan nukiliya a Dutsen Kolang, bayan da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar kai hari kan wurin da ke tsakiyar ƙasar.
Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmaeil Baqaei, ya bayyana hakan a shafinsa na X a ranar Laraba cewa, “Yawan mayar da hankali da Washington ke yi kan Kolang Kouh, inda babu wani aikin nukiliya da ake gudanarwa, ba komai ba ne face wata hujja ta ƙarya da aka ƙirƙira domin kai hari, lalata abubuwa da kuma cigaba da tada zaune tsaye.”
Ya kuma jaddada cewa Iran ta bayyana dukkan ayyukanta na nukiliya ga Hukumar Kula da Makaman Nukiliya ta Majalisar Ɗinkin Duniya (IAEA).
A ranar Talata, Trump ya yi barazanar cewa Amurka za ta kai hari kan wurin, wanda ake kira Pickaxe Mountain da Turanci.
A shekarar 2025, wasu manyan kafafen yaɗa labarai na Amurka, ciki har da The Washington Post da The New York Times, sun ruwaito cewa Iran ta hanzarta aikin gina wani ɓoyayyiyar cibiyar nukiliya ta ƙarƙashin ƙasa a Dutsen Kolang. Sai dai Tehran ta musanta rahotannin.
Dutsen Kolang na kusa da cibiyar nukiliyar Natanz ta Iran, wadda Amurka ta kai wa hari a lokacin wani taƙaitaccen yaƙi da aka yi a watan Yunin shekarar 2025.














