Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai jagoranci tawagar Nijeriya zuwa Indiya, domin halartar taron shugabannin ƙasashen BRICS karo na 18 da za a gudanar a birnin New Delhi daga 12 zuwa 13 ga Satumba 2026.
Nijeriya, wadda ke cikin ƙasashe abokan hulɗar BRICS, za ta shiga cikin taron da ke haɗa manyan ƙasashe masu tasowa domin tattauna batutuwan tattalin arziƙi, da kasuwanci, da shugabanci na duniya da sauran batutuwan da suka shafi ƙasashe masu tasowa.
Taron na bana zai gudana ne a ƙarƙashin jagorancin Indiya, wadda ke riƙe da shugabancin BRICS a shekarar 2026. Ana kuma sa ran shugabannin ƙasashe da manyan jami’ai daga ƙasashen BRICS da abokan hulɗarsu za su halarta, ciki har da Shugaban Rasha Vladimir Putin, da Shugaban China Xi Jinping da Shugaban Iran Masoud Pezeshkian.
A yayin taron, ana sa ran za a tattauna hanyoyin ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziƙi, da rage dogaro da tsarin kuɗin duniya da ake amfani da shi yanzu, da bunƙasa kasuwanci da kuma ƙarfafa matsayin ƙasashe masu tasowa a harkokin duniya.
Halartar Shettima a madadin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na zuwa ne yayin da Nijeriya ke ƙara taka rawa a cikin tsarin BRICS, bayan ta samu matsayin ƙasar abokiyar hulɗa, tare da fatan ƙarfafa dangantakarta da Indiya da sauran ƙasashen ƙungiyar.














