Mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bukaci tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya janye daga takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027, tare da goyon bayan tikitin NDC.
Kwankwaso ya yi wannan kira ne yayin da yake ganawa da mambobin Ƙungiyar Manoma Fulani a gidansa da ke Abuja. Ya ce ya kamata Atiku ya yi la’akari da shekarunsa da kuma lafiyarsa, ya mayar da hankali kan ayyukan sarauta da ke tattare da matsayinsa na Wazirin Adamawa.
Ya kuma roƙi mutanen Adamawa da su je wajen Atiku su shawo kansa ya janye daga takarar. Kwankwaso ya ce idan shi da Peter Obi suka samu nasarar lashe zaɓen shugaban ƙasa, za su kula da Atiku yadda ya kamata.
Atiku, wanda ke neman tikitin jam’iyyar ADC domin takarar 2027, ya sha tsayawa takarar shugaban ƙasa a baya. A watan Afrilu ya ce zaɓen 2027 na iya zama yunƙurinsa na karshe na neman shugabancin ƙasar.
Kalaman Kwankwaso na zuwa ne a lokacin da manyan ’yan adawa ke ci gaba da ƙoƙarin sake tsara sabon kawance domin tunkarar zaɓen 2027, yayin da shi da Peter Obi ke wakiltar NDC, Atiku kuma ke neman shugabancin ƙasa a ƙarƙashin ADC.













