Jakadan kasar Sin a jamhuriyar Nijar Lv Guijun, ya tattauna da kungiyar musulmin jamhuriyar Nijar a jiya Asabar, yayin bikin mika babban masallacin birnin Yamai da aka yiwa kwaskwarima. Bikin ya samu halartar shugabannin kungiyar musulmin jamhuriyar Nijar da sauran mazauna birnin.
Yayin bikin, Lv ya gabatar da manufar cikakken taro na hudu, na kwamitin kolin JKS na 20, da shawarar kasa da kasa ta wayewar kai da kasar Sin ta gabatar, ga shugabannin addinin musulunci na Nijar, ya kuma fayyace manufofin addini na Sin. Kazalika, ya bayyana fatan jagororin addini a Nijar, za su taimaka wajen yaukaka kawance tsakanin Sin da Nijar.
A nasa tsokaci, shugaban kungiyar musulmi ta Nijar, ya gabatar da masallacin, da ma halin da musulmin Nijar suke ga jakada Lv, yana mai jinjinawa kwazon da gwamnatin Sin ke yi wajen martabawa, da kare ‘yancin bin addinai. Kana ya bayyana aniyar wanzar da kawancen gargajiya tsakanin Nijar da Sin, tare da zurfafa musaya da hadin gwiwa tsakanin sassan biyu. (Saminu Alhassan)














