Ƙasashen Birtaniya (UK) da Tarayyar Nijeriya, a ranar Talata, sun ƙulla tare da sabunta wata yarjejeniya mai ƙarfi domin yaƙi da hanyoyin samar da kuɗaɗen ta’addanci, barazanar intanet, yaɗuwar labaran ƙarya, da sauran sabbin ƙalubalen tsaro da ke kunno kai.
Wannan gagarumin taro ya gudana ne a Ofishin Mai Ba Gwamnati Shawara kan Tsaron Ƙasa (NSA) da ke Abuja, yayin buɗe taron tattaunawa karo na huɗu (4) kan haɗin gwiwar tsaro da kariya tsakanin UK da Nijeriya, wanda aka gudanar a gaban mutum fiye da mutum 20 ƴan ƙasar Birtaniya.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, wannan taro da aka gudanar ƙarƙashin sabon tsarin tsaro na UK da Nijeriya, ya samu halartar shugabannin hukumomin tsaro da na kariya, da suka haɗa da Babban Jami’in Tsaron Ƙasa Janar Olufemi Oluyede, da sauran shugabannin rundunonin soji, gami da jami’an diflomasiyya na ƙasashen biyu.
Yayin da yake jawabi kafin a tafi zaman sirri, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro na Ƙasa, Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa wannan ƙawance ya canza zuwa babban tsari na musamman da ya shafi yaƙi da ta’addanci, tsaron intanet, tabbatar da kwanciyar hankali a yankuna, martani ga lokutan ɓacin rana, tsaron ruwa, da kuma musayar bayanan sirri.
Ribadu ya bayyana cewa wannan zama yana zuwa ne a daidai lokacin da yanayin tsaron duniya ke ƙara rikicewa, inda tsofaffin barazana ke sauyawa tare da gaurayuwa da sabbin ƙalubale na fasahar zamani.
Ya ce: “Ta’addanci, tsattsauran ra’ayi na tashin hankali, laifukan intanet, rukunonin miyagu da suka shirya kansu, zirga-zirgar kuɗaɗen haram, da maguɗin labarai na ƙasashen waje suna buƙatar matakin haɗin gwiwa da ba a taɓa gani ba tsakanin abokan hulɗa da aka amince da su.”
“Babu wata ƙasa da za ta iya tunkurar waɗannan barazana ita kaɗai. Samun sahihin martani yana buƙatar haɗin gwiwa a fannonin tsaro, leƙen asiri, tilasta bin doka, diflomasiyya, ƙarfin yanar gizo, da makaman tattalin arziki,” in ji NSA.
Ya jaddada cewa Nijeriya za ta ci gaba da taka rawar gani a matsayin jagoriyar tsaro a Afirka ta hanyar inganta zaman lafiya, mulkin demokraɗiyya, da juriya ta bai daya. Ya kuma gode wa UK bisa goyon bayan da take ba wa Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) na Nijeriya.
A nasa ɓangaren, Mai Bai Wa Gwamnatin Birtaniya Shawara kan Tsaron Ƙasa, Jonathan Powell, ya bayyana Nijeriya a matsayin babbar abokiyar ƙawancen Birtaniya a duk faɗin Afirka, kuma jigo wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin da ma tsaro na bai ɗaya.
Powell ya bayyana cewa barazanar zamani ta kasance mai sarƙaƙiya da ke haɗe da juna, wanda hakan ke buƙatar ƙasashe su canza takunsu tare da yin aiki kafaɗa-da-kafaɗa.
Ya ce: “Muna fuskantar zamanin barazana na gauraye. Ta’addanci, laifukan intanet, labaran ƙarya, kuɗaɗen haram, shiriryayyen laifi, da hare-hare kan manyan gine-ginen gwamnati suna ƙara alaƙa da juna. Waɗannan ƙalubale suna buƙatar mu sake tsarinmu mu yi aiki tare fiye da kowane lokaci.”
Muhimman sassan tallafin na Birtaniya ga Nijeriya:
Taimakon Soji Na Gaba-da-Gaba: Powell ya bayyana cewa a halin yanzu akwai dakarun sojin Birtaniya da ke taimaka wa sojojin Nijeriya a garin Maiduguri.
Yakar Labaran Karya (Disinformation): Powell ya nuna cewa labaran ƙarya sun zama ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da ke fuskantar tsarin demokraɗiyya a yau, domin suna iya gurgunta amincin hukumomi, haɗa rarrabuwar kai a al’umma, da raunana haɗin kan ƙasa.
Katse Kuɗaɗen Ta’addanci: Ƙasashen biyu sun amince da yaƙi da hanyoyin sadarwa na kuɗaɗen haram da ke rura wutar ta’addanci da rashin daidaito.
Ana sa ran wannan tattaunawa za ta duba irin ci gaban da aka samu ƙarƙashin yarjejeniyar tsaro ta ƙasashen biyu, sannan a gano sabbin fannoni na haɗin gwiwa domin murƙushe sabbin barazanar da ke tasowa.














