Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin gudanarwa na musamman domin gudanar da bincike mai zurfi kan silar mutuwar wata ɗaliba a makarantar St. Louis College da ke Kano. Wannan mataki na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da Kwamishinan Ƴansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya kafa tasa rundunar binciken kan mutuwar ɗalibar mai suna Maimuna Sani Salisu, wadda ke aji biyu na babban sashin kwana na sakandaren.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar, ya bayyana cewa kwamitin gwamnatin jihar zai gudanar da bincike mai zaman kansa cikin adalci da ƙwarewa.
Sanarwar ta nuna cewa Kwamishinan Ilimi na Jihar, Gwani Alhaji Ali Haruna Makoda, shi ne zai jagoranci kwamitin, tare da taimakon sauran mambobin da suka haɗa da ƙwararrun Alkalai, da jami’an ilimi, da wakilin ƙungiyar iyaye da malamai (PTA).
An umarci kwamitin da ya gano ainihin yadda abubuwa suka faru da kuma binciko ko akwai gazawa wajen kulawa, da gudanarwa, ko tsare-tsaren makarantar da suka yi sanadiyyar mutuwar ɗalibar.
Haka zalika, aikin kwamitin ya haɗa da duba rahotannin lafiya, da bincikar yanayin zamantakewar makarantar, da kuma binciken zargi na cin zarafi (bullying), da tilastawa, ko kuma amfani da hanyoyin ladabtarwa da ba su dace ba a tsakanin ɗalibai.
Gwamna Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an gano gaskiyar lamarin domin tabbatar da adalci da kuma ɗaukar matakan da suka dace don kauce wa faruwar hakan a nan gaba. Ana sa ran kwamitin zai kammala bincikensa ya mika rahoto ga gwamnati nan ba da daɗewa ba, yayin da su ma jami’an ƴansanda ke ci gaba da nasu binciken a gefe guda.














