ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

by Abubakar Sulaiman
1 day ago

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin gudanarwa na musamman domin gudanar da bincike mai zurfi kan silar mutuwar wata ɗaliba a makarantar St. Louis College da ke Kano. Wannan mataki na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da Kwamishinan Ƴansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya kafa tasa rundunar binciken kan mutuwar ɗalibar mai suna Maimuna Sani Salisu, wadda ke aji biyu na babban sashin kwana na sakandaren.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar, ya bayyana cewa kwamitin gwamnatin jihar zai gudanar da bincike mai zaman kansa cikin adalci da ƙwarewa.

Sanarwar ta nuna cewa Kwamishinan Ilimi na Jihar, Gwani Alhaji Ali Haruna Makoda, shi ne zai jagoranci kwamitin, tare da taimakon sauran mambobin da suka haɗa da ƙwararrun Alkalai, da jami’an ilimi, da wakilin ƙungiyar iyaye da malamai (PTA).

ADVERTISEMENT

An umarci kwamitin da ya gano ainihin yadda abubuwa suka faru da kuma binciko ko akwai gazawa wajen kulawa, da gudanarwa, ko tsare-tsaren makarantar da suka yi sanadiyyar mutuwar ɗalibar.

Haka zalika, aikin kwamitin ya haɗa da duba rahotannin lafiya, da bincikar yanayin zamantakewar makarantar, da kuma binciken zargi na cin zarafi (bullying), da tilastawa, ko kuma amfani da hanyoyin ladabtarwa da ba su dace ba a tsakanin ɗalibai.

LABARAI MASU NASABA

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

Gwamna Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an gano gaskiyar lamarin domin tabbatar da adalci da kuma ɗaukar matakan da suka dace don kauce wa faruwar hakan a nan gaba. Ana sa ran kwamitin zai kammala bincikensa ya mika rahoto ga gwamnati nan ba da daɗewa ba, yayin da su ma jami’an ƴansanda ke ci gaba da nasu binciken a gefe guda.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
  • Abubakar Sulaiman
    Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

MASU ALAKA

Labarai

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
Labarai

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Next Post
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

LABARAI MASU NASABA

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.