An kaddamar da cibiyar horar da ma’aikatan jinya ta kasashen Sin da Saliyo, a asibitin sada zumunta na Saliyo da Sin dake birnin Freetown, a ranar Juma’ar da ta gabata. Tawagar jami’an lafiya ta Sin ta 27 ce za ta jagoranci ayyukan cibiyar, wadda za ta zamo dandalin dindindin na ilmantar da ma’aikatan jinya, da samar da horon sanin makamar aiki tsakanin kasashen biyu.
Da yake tsokaci game da hakan, mataimakin ministan lafiya na daya na kasar Saliyo Charles Senessie, ya jinjinawa tallafin tsawon lokaci da Sin ke samarwa Saliyo, yana mai cewa cibiyar za ta cike gibin kamfar ilimin aikin jinya, ta hanyar koyar da dabarun zamani na kiwon lafiya da kwarewa ga jami’an lafiyar kasar.
A nasa tsokacin kuwa, shugaban tawagar ta Sin Li Zheng, cewa ya yi cibiyar tamkar dan ba ce ta sauyin da ake fata, daga bayar da tallafin kiwon lafiya na gajeren zango, zuwa cikakken tsarin samar da kwarewa a fannin, kana za ta kafa wani ginshiki mai nagarta, a fannin wanzar da hadin gwiwar inganta kiwon lafiya tsakanin Sin da Saliyo.
Sama da ma’aikatan jinya 40 ne suka fara halartar kwas din farko na watanni biyu da cibiyar ta kaddamar. Kuma rahotanni na cewa ma’aikatan dake samun horon sun fito ne daga manyan asibitocin kasar guda biyar. (Saminu Alhassan)














