ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman Takaichi Masu Matukar Ban-Takaici

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Takaichi

A kwanan ne ne firaminista Sanae Takaichi ta kasar Japan ta tsaya a gaban kyamarori yayin wani zama a majalisar dokokin kasar, ta furta wasu kalamai na katobara masu ban-takaici, kan cewa, matukar kasar Sin ta dauki matakin soji a kan yankin Taiwan, hakan zai zama barazana ga dorewar kasar ta Japan. Wannan katobara ta watsu tamkar wutar daji a duk fadin yankin Asiya, har ma da sauran sassan kasa da kasa, bisa yadda ta kunshi tsokana da kuma neman tayar da zaune-tsaye a sabon zamani.

Ga wadanda za su iya tunawa da tarihi, sun san ba wannan ne karon farko da Japan ta saba yin kasassaba ba. A cikin manyan kaba’irorin da ta tafka, ta yi amfani da kalmar “kare kai” da “tabbatar da tsaro” wajen kaddamar da munanan farmakin soji. A cikin shekarun 1930 da 1940, shugabannin kasar sun ba da hujjar cin zarafi da aika-aikar da suka tafka a Manchuria ta kasar Sin, da sauran sassan yankin Pacific, a matsayin wai “kokarin kare dorewar kasar Japan”. Ta aikata mummunan zalunci na kisan gilla a Nanjing, da sauran bala’o’in da ta haddasa a yankin Asiya, har dai daga bisani ta ga iyakar kanta a shekarar 1945.

Katobarar Takaichi, duk da cewa ta furta ce a cikin wannan karni na 21, amma tana dauke da sako iri daya da wadda aka taba furtawa a kasar lokacin mulkin danniya. Ta danganta makomar Taiwan kai-tsaye da dorewar kasar Japan, inda hakan ke nuna kasadar da take neman yi a kan sake farfado da tunanin Japan na mamaye makwabtanta maimakon zama tare cikin lumana.

ADVERTISEMENT

Ganin irin hadarin dake tattare da katobarar Takaichi musamman wajen kawo cikas ga zaman lafiyar da ake ta kokarin karfafawa a yankin Asiya, kasar Sin ba ta bata lokaci ba wajen yin Allah wadai da katobarar tata, tare da mayar da zazzafan martani ta hanyoyin da suka dace a ciki da wajen kasar.

Yanzu haka, Sinawa da dama sun suka soke tafiye-tafiye zuwa Japan baki daya, lamarin da ke kawo cikas ga bunkasar tattalin arzikin kasar ta Japan, kasancewar matakin na Sinawa zai iya haifar wa kasar da asarar adadin da ya kai kudin kasar JYE tiriliyan 2.2, kwatankwacin kudin Sin yuan biliyan 101.6, kamar yadda aka ji daga wani masani a kwalejin bincike ta Nomura Takahide Kiuchi. Kuma wannan fa, baya ga asarar da za ta tafka ce a bangaren cinikayya da kasar Sin, wanda ko a bara, adadin kasuwancin da aka yi a tsakanin kasashen biyu ya kai dalar Amurka biliyan 308.3.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Tarihi dai ba ya karya kuma ya kamata ya zama madubi ga firaminista Takaichi wajen yin waiwaye a kan shugabannin da suka gabace ta wadanda suka kai kasar suka baro. Kazalika, matukar kasar na son zama wani sabon karfi mai matukar fada-a-ji a yankin Asiya, ta bi hanyoyin lumana da kyautata mu’amala maimakon fito-na-fito da tayar da fitina.

Hakika dai, kalaman Takaichi na da matukar ban-takaici! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Takaichi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
Takaichi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
An Yi Wa Sojoji Kwanton Ɓauna Yayin Da Suke Bin Sahun Ɗalibai Mata Da Aka Sace A Kebbi

An Yi Wa Sojoji Kwanton Ɓauna Yayin Da Suke Bin Sahun Ɗalibai Mata Da Aka Sace A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.