ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalaman Takaichi Masu Matukar Ban-Takaici

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Takaichi

A kwanan ne ne firaminista Sanae Takaichi ta kasar Japan ta tsaya a gaban kyamarori yayin wani zama a majalisar dokokin kasar, ta furta wasu kalamai na katobara masu ban-takaici, kan cewa, matukar kasar Sin ta dauki matakin soji a kan yankin Taiwan, hakan zai zama barazana ga dorewar kasar ta Japan. Wannan katobara ta watsu tamkar wutar daji a duk fadin yankin Asiya, har ma da sauran sassan kasa da kasa, bisa yadda ta kunshi tsokana da kuma neman tayar da zaune-tsaye a sabon zamani.

Ga wadanda za su iya tunawa da tarihi, sun san ba wannan ne karon farko da Japan ta saba yin kasassaba ba. A cikin manyan kaba’irorin da ta tafka, ta yi amfani da kalmar “kare kai” da “tabbatar da tsaro” wajen kaddamar da munanan farmakin soji. A cikin shekarun 1930 da 1940, shugabannin kasar sun ba da hujjar cin zarafi da aika-aikar da suka tafka a Manchuria ta kasar Sin, da sauran sassan yankin Pacific, a matsayin wai “kokarin kare dorewar kasar Japan”. Ta aikata mummunan zalunci na kisan gilla a Nanjing, da sauran bala’o’in da ta haddasa a yankin Asiya, har dai daga bisani ta ga iyakar kanta a shekarar 1945.

Katobarar Takaichi, duk da cewa ta furta ce a cikin wannan karni na 21, amma tana dauke da sako iri daya da wadda aka taba furtawa a kasar lokacin mulkin danniya. Ta danganta makomar Taiwan kai-tsaye da dorewar kasar Japan, inda hakan ke nuna kasadar da take neman yi a kan sake farfado da tunanin Japan na mamaye makwabtanta maimakon zama tare cikin lumana.

ADVERTISEMENT

Ganin irin hadarin dake tattare da katobarar Takaichi musamman wajen kawo cikas ga zaman lafiyar da ake ta kokarin karfafawa a yankin Asiya, kasar Sin ba ta bata lokaci ba wajen yin Allah wadai da katobarar tata, tare da mayar da zazzafan martani ta hanyoyin da suka dace a ciki da wajen kasar.

Yanzu haka, Sinawa da dama sun suka soke tafiye-tafiye zuwa Japan baki daya, lamarin da ke kawo cikas ga bunkasar tattalin arzikin kasar ta Japan, kasancewar matakin na Sinawa zai iya haifar wa kasar da asarar adadin da ya kai kudin kasar JYE tiriliyan 2.2, kwatankwacin kudin Sin yuan biliyan 101.6, kamar yadda aka ji daga wani masani a kwalejin bincike ta Nomura Takahide Kiuchi. Kuma wannan fa, baya ga asarar da za ta tafka ce a bangaren cinikayya da kasar Sin, wanda ko a bara, adadin kasuwancin da aka yi a tsakanin kasashen biyu ya kai dalar Amurka biliyan 308.3.

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Tarihi dai ba ya karya kuma ya kamata ya zama madubi ga firaminista Takaichi wajen yin waiwaye a kan shugabannin da suka gabace ta wadanda suka kai kasar suka baro. Kazalika, matukar kasar na son zama wani sabon karfi mai matukar fada-a-ji a yankin Asiya, ta bi hanyoyin lumana da kyautata mu’amala maimakon fito-na-fito da tayar da fitina.

Hakika dai, kalaman Takaichi na da matukar ban-takaici! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Takaichi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Takaichi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
Daga Birnin Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
Daga Birnin Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
Next Post
An Yi Wa Sojoji Kwanton Ɓauna Yayin Da Suke Bin Sahun Ɗalibai Mata Da Aka Sace A Kebbi

An Yi Wa Sojoji Kwanton Ɓauna Yayin Da Suke Bin Sahun Ɗalibai Mata Da Aka Sace A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.