Kasar Sin ta bayyana rashin gamsuwa da adawa mai karfi ga matakin ma’aikatar tsaron Amurka na sanya kamfanoni da dama na Sinawa, cikin kamfanoni masu alaka da ayyukan soji.Kakakin ma’aikatar kula da harkokin cinikayya na kasar Sin ne ya bayyana haka a yau Asabar, inda ya ce Amurka na watsi da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin ganawarsu a Beijing, da kuma yin ko in kula da dukkan muradun dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, yana cewa, bangaren Amurka na ci gaba da amfani da batun tsaron kasa kan komai da amfani da matsayinsa ba bisa ka’ida ba, wajen danne kamfanonin kasar Sin ba tare da hujja ba.
Ya ce irin wadannan matakai na Amurka na matukar illa ga tsarin cinikayya da tattalin arziki na duniya, da barazana ga tsarin ayyukan masana’antu da na samar da kayayyaki na duniya, tare da illata halaltattun hakkoki da muradun kamfanonin kasar Sin.
A cewar kakakin, kasar Sin na bukatar Amurka ta gaggauta dakatar da munanan ayyukanta, da janye matakan nata ba tare da bata lokaci ba, kana ta koma ga daidaitacciyar turbar gina dangantakar Sin da Amurka mai ma’ana da muhimmanci. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post