Kasar Sin ta fitar da shirin kai wa matakin koli na fitar da hayakin Carbon yayin wa’adin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 daga shekarar 2026 zuwa ta 2030, wanda ya zayyana taswirar cimma burinta na kai wa matakin koli na fitar da hayakin Carbon kafin shekarar 2030 yayin da take gaggauta komawa ga makamashi mai tsafta.
Zuwa shekarar 2030, shirin ya tsara rage fitar da hayakin carbon kan makin GDP da kaso 17 daga matakan da yake kai a shekarar 2025.
Haka kuma, yana da nufin kara kason makamashi mai tsafta cikin jimilar makamashin da ake amfani da shi zuwa kaso 25, ya zuwa 2030. (Fa’iza Mustapha)
ADVERTISEMENT
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/













