Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sake zaɓar Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa a zaɓen shekarar 2027.
Wannan mataki ya kawo ƙarshen jita-jitar da aka daɗe ana yi cewar Tinubu na iya sauya mataimakinsa saboda wasu dalilai na siyasa.
A ranar Juma’a, Ibrahim Masari, mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin siyasa, ya miƙa takardun tsayawar takarar Tinubu da Shettima ga shugabannin jam’iyyar APC a Abuja.
Taron ya samu halartar wasu gwamnonin APC, shugabannin jam’iyya, ’yan majalisar tarayya da sauran masu ruwa da tsaki.
Miƙa takardun ya tabbatar da cewa Tinubu zai nemi wa’adi na biyu a ƙarƙashin APC tare da Shettima a matsayin abokin takararsa.
Sunday Dare, mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai da sadarwa, shi ma ya tabbatar da hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce Tinubu ya zaɓi Shettima a matsayin abokin takararsa a zaɓen 2027.














