A yau Juma’a ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta yi watsi da zargin da wasu kafofin watsa labarai na kasashen waje ke yiwa kasar Sin, na cewa wai “Tana takure damar” ci gaban sauran kasashe masu tasowa.
A baya-bayan nan, wasu kafofin yada labaru na kasashen waje sun rika yada karairayi, da zargin cewa wai masana’antun kasar Sin, baya ga girgiza kasuwannin yammacin duniya da suke yi, a daya bangaren suna kuma toshe damar da ya kamata kasashe masu tasowa su samu. Game da hakan, yayin taron manema labarai da ya gudana a yau, Mao Ning ta jaddada cewa, wannan zargi ne da ya sabawa gaskiya, kuma su kansu kasashe masu tasowa ba za su amince da shi ba.
Mao ta kara da cewa, a matsayinta na membar kasashe masu tasowa, har kullum kasar Sin na raba dabarunta na neman ci gaba ba tare da boye komai ba, tana kuma taimakawa wajen ingiza ci gaban kasashe masu tasowa. Har ila yau, bisa nasarorin da take samu karkashin matakan hadin gwiwa a fannin samar da ababen more rayuwa, da zuba jari, da fasahohi, Sin ta taimakawa kasashe masu tasowa, da damar gina kwarewar aiki don samun ci gaba.
Kazalika, ta hanyar bude kasuwanninta, Sin ta taimakawa kasashe masu tasowa da damar fadada shigar da hajojinsu masu inganci zuwa cikin kasar, wanda hakan ya bunkasa masana’antunsu da kudaden shiga. Bugu da kari, ta hanyar samar da zarafi, da hajoji marasa gurbata yanayi masu rahusa, Sin ta taimakawa kasashe masu tasowa, da damar inganta samun kudaden shiga, da gaggauta sauyi, da daga matsayin masana’antunsu.
Dukkanin wadannan sun shaida yadda Sin da sauran kasashe masu tasowa, ke zama abokan tafiya ta fannin neman cimma nasarar zamanantarwa. (Saminu Alhassan)














