ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
42 seconds ago
Afirka

Ci gaban bangaren kimiyya da fasaha ya kasance tamkar “kashin baya” ga wata kasa. Dole ne a samu kashin baya mai karfi, kafin daga bisani kasar ta iya kawar da shingen da ya hana ta samun ci gaba mai dorewa a bangaren tattalin arziki. 

A kwanan nan, an gudanar da babban taron shekara-shekara na karrama masu nazarin kimiyya da fasaha a kasar Sin, inda mutane biyu suka samu lambobin yabo na matsayin koli, kana masana kimiyya da fasaha masu gudanar da wasu ayyuka 258 su ma sun samu lambobin yabo. Wadannan ayyuka sun shafi ilimin wasu bangarori na tushe, wadanda ke samar da taimako wajen biyan bukatar kasar Sin ta raya wasu manyan tsare-tsare, ko kuma haifar da alfanu ga al’ummar kasar. 

A wajen taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping da kansa ya mika lambobin yabon ga mutanen da aka karrama, kana ya yi wani jawabi, inda ya bukaci a karfafa hadin gwiwa tsakanin sassa da hukumomi na Sin a fannin kirkiro sabbin fasahohi, da inganta cudanya tsakanin bangarorin nazarin kimiyya da fasaha da masana’antu, da kara kokarin horar da matasa, da kyautata tsarin kula da kimiyya da fasaha da tabbatar da tsaro, da dai sauransu. 

ADVERTISEMENT

Jawabin shugaba Xi ya nuna yadda shugabannin kasar Sin suke fahimtar batun nazarin kimiyya da fasaha, da jagoranci mai nagarta da suke samarwa a wannan fanni. 

To, sai dai, wane tasiri ci gaban bangaren kimiyya da fasaha na kasar Sin ke da shi ga duniya, musamman ma kasashen Afirka? 

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Dangane da wannan tambaya, wani jami’i mai kula da harkokin waje na kasar Najeriya mai suna Raymond Delmut ya ba da amsa, ta hanyar rubuta wata makala, wadda aka wallafa a shafin yanar gizo na jaridar “the Sun” ta Najeriya. Cikin bayaninsa, Mista Delmut ya ce, yanzu haka kasar Sin na sauya salonta daga “mai samar da hajoji” zuwa “mai kirkiro sabbin fasahohi”. Saboda haka salon hadin gwiwar Sin da Afirka shi ma zai sauya, daga mai dogaro kan aikin gini da ciniki, zuwa nau’in da zai fi dora muhimmanci kan kirkire-kirkire, da ci gaban masana’antu, da musayar ilimi. A cewarsa, ci gaban bangaren kimiyya da fasaha na kasar Sin dama ce ga kasashe masu tasowa ta raya tattalin arziki, maimakon barazanar takara. 

Hakika, ta hanyar tantance sakamakon da aka samu a kasashen Afirka, bisa hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin kimiyya da fasaha, cikin sauki za mu iya fahimtar nagartaccen tasirin da kasar Sin ta yi. 

Misali, a Najeriya, wasu kwararru masu ilimin aikin gona na kasar Sin sun kirkiro wani sabon nau’in shinkafa, wanda ya sa yawan shinkafar da a kan girba cikin gonar da fadinta ya kai eka 1, ya karu daga ton 5.6 zuwa ton 8. Kana a kasar Morocco, tashar samar da wutar lantarki ta makamashin hasken rana da wani kamfanin kasar Sin ya gina tana samar da wutar lantarki mai tsabta ga miliyoyin magidanta. Ban da haka, cibiyar tattara alkaluman labarin kasa ta Sin da Afirka tana samar da hidimar gargadin kare kai daga bala’u ga kasashe 54 dake nahiyar Afirka, yayin da sabon tsarin biyan kudi na zamani da aka gina a tsakanin bangarorin Sin da Afirka ya sa abun da ake kashewa wajen biyan kudi yayin gudanar da ciniki raguwa da fiye da kaso 30%. Haka zalika, allunan sola kirar kasar Sin suna samar da damar amfani da wutar lantarki ga karin mutane a sassa daban daban na nahiyar Afirka. 

Ta wadannan misalai za mu san cewa, “kashin bayan” kimiyya da fasaha na kasar Sin ya riga ya zame wa kasashen Afirka abin dogara. (Bello Wang) 

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing
  • Sulaiman
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Sulaiman
    Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin
  • Sulaiman
    Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

MASU ALAKA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sana’ar Ɗinki: Yadda Telolin Zariya Suka Yi Fice A Sassan Afirka

July 10, 2026
Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

July 10, 2026
Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

July 10, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.