Fadar Shugaban Ƙasa ta sanar da cewa an ceto dukkanin ɗalibai da malaman da aka sace a ƙaramar hukumar Orire da ke Jihar Oyo bayan shafe makonni a hannun maharan da suka sace su.
Mai magana da yawun Shugaba Bola Tinubu, Bayo Onanuga ne, ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a yammacin ranar Juma’a.
“Daga ƙarshe, an ceto dukkanin ɗalibai da malaman da aka sace a Orire, Oyo, ta hannun jami’an tsaronmu,” in ji Onanuga.
An sace waɗanda abin ya shafa ne a ranar 15 ga watan Mayu, 2026, bayan wasu ’yan bindiga sun kai hari wata makaranta da ke ƙaramar hukumar Orire, inda suka kashe wani malami tare da yin awon gaba da ɗalibai da wasu ma’aikatan makarantar.
Bayan faruwar lamarin, jami’an tsaro sun ƙaddamar da aikin ceto domin ku5butar da waɗanda aka sace, inda rundunar soji da sauran hukumomin tsaro suka shiga aikin.
A yayin da ake gudanar da aikin ceto su, Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayyana cewa sojoji na taka-tsantsan domin tabbatar da cewa rayukan waɗanda aka sace ba su shiga hatasri ba yayin gudanar da aikin.
Sai dai Bayo Onanuga bai yi ƙarin bayani kan yadda aka gudanar da aikin ceto su ba ko kuma halin da waɗanda aka ceto suke ciki.
Hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan yadda aka ceto su hae zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.



















