ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

by CMG Hausa
3 years ago
taro

Da tsakar ranar jiya agogon wurin ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci kwarya-kwaryar taron tattaunawa da kuma liyafar cin abincin rana tsakanin shugabannin mambobin kungiyar APEC da baki da suka karbi bakuncinsu a San Francisco na kasar Amurka.

A yayin taron, Xi Jinping ya nuna cewa, a ’yan shekarun baya-bayan nan, kungiyar APEC ta kara karfin tabbatar da manufofin Putrajaya nan da shekaru 2040, da kuma tabbatar da manufofin Bangkok na samun ci gaban tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, ta yadda za a taka rawa a bangaren samun bunkasuwa a duniya ba tare da gurbata muhalli ba. A bisa halin da ake ciki yanzu, kamata ya yi, kasashe daban-daban su kai ga cimma matsaya daya da daukar mataki tare, don ba da gudunmawarsu a wannan fanni. Kan haka Xi Jinping ya ba da shawarwari guda uku:

Na farko, gaggauta tabbatar da ajandar samun ci gaba mai dorewa ta MDD nan da shekarar 2030. Kana Sin kuma ta gabatar da shawararin samun bunkasuwar duniya, wanda zai taka rawa wajen karawa kasashen duniya kwarin gwiwar hada kai don tinkarar gibin da ake samu ta fuskar ci gaban tattalin arziki.

ADVERTISEMENT

Na biyu, a fito da wata sabuwar hanyar samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, ta yadda za a kafa wani yanayi mai adalci tsakanin bunkasuwar tattalin arziki da kiyaye muhalli.

Na uku, hadin kan kasashen duniya wajen tinkarar sauyin yanayi. Kiyaye yarjejeniyar MDD kan sauyin yanayi a matsayin babbar hanyar tafiyar da harkoki masu alaka da yanayin duniya. Da magance matsalolin da ke damun kasashe masu tasowa ta fuskar kudade, inganta kwarewa da musayar fasahohi, ta yadda za a tabbatar da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi na MDD da ta Paris.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ban da wannan kuma, Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin tana kokarin tabbatar da shawarar “ziri daya da hanya daya” a bangare kiyaye muhalli, za kuma ta ci gaba da gina manyan ababen more rayuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da samar da tsabtaccen makamashi da amfani da shi a fannin zirga-zirga. Sin na fatan hada kai da bangarori daban-daban don kara ba da gudunmawa wajen gina kyakkyawar makomar Bil Adama ta bai daya na samun bunkasuwa tare, da samar da yanayi mai kyau a duniya.

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ne ya jagoranci wannan taro mai taken “Samun bunkasuwa mai dorewa da lura da sauyin yanayi da zamanintar da makamashi.”
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi shi ma ya halarci wannan taro.(Amina Xu)

  • Xi Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Liyafar Da Aka Shirya Masa A San Francisco
taro
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Liyafar Da Aka Shirya Masa A San Francisco

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.