Yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sanar da sanya takunkumi kan ministan tsaron kasar Philippines, Gilberto Teodoro Jr. da iyalansa.Kakakin ya ce, Gilberto Teodoro Jr. ya sha yin kalaman da ba su dace ba a kan kasar Sin, wadanda suka lalata halastattun muradun kasar Sin da ma huldar da ke tsakanin kasashen biyu.
Don kiyaye ikon mulkin kai da ma tsaro da muradunta, kasar Sin ta yanke shawarar hana Gilberto Teodoro Jr. da uwargidansa da ma yaransa zuwa babban yankin kasar Sin da kuma yankunan Hong Kong da Macao na kasar, tare da haramta wa kungiyoyi da daidaikun mutane na cikin kasar Sin yin kowane irin nau’i na ciniki ko hadin gwiwa da Gilberto Teodoro Jr. da uwargidansa da kuma yaransa.














Discussion about this post