A gabar da ake gudanar da dandalin kasa da kasa game da tsarin jagorancin hakkin dan Adam na shekarar nan ta 2026, kafar CGTN ta kasar Sin da hadin gwiwar da jami’ar Renmin ta kasar, sun gudanar da binciken jin ra’ayoyin al’ummun kasa da kasa, inda masu bayyana ra’ayoyi 12,000 daga kasashe 43 suka bayyana gamsuwa da irin manyan nasarori da kasar Sin ta cimma a fannin hakkin dan Adam.
Sakamakon binciken ya nuna yadda kaso sama da 60 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin, suka jinjinawa nasarorin kasar Sin a fannoni takwas na jagoranci, wadanda suka hada da samar da ababen more rayuwa, da daga matsayin ilimi, da ayyukan yi, da kudaden shigar jama’a, da yanayin muhallin rayuwa, da kiwon lafiya, da tsaron al’umma da kare muhallin halittu.
Bisa rukunonin shekarun haihuwa kuwa, masu bayyana ra’ayoyin ‘yan kasa da shekaru 45 a duniya, sun bayyana gamsuwa da ta haura kaso 80 bisa dari ga tsarin jagorancin hakkin dan Adam na Sin, a fannonin samar da ababen more rayuwa da raya ilimi, yayin da gamsuwar ‘yan tsakanin shekaru 18 zuwa 24 ta haura zuwa kaso 83.6 bisa dari a bangaren samar da ababen more rayuwa da kaso 85.9 bisa dari a fannin raya ilimi. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post