Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a yau Lahadi cewa, bisa la’akari da karuwar farfado da karfin soja a Japan da zama barazana ta hakika, abu ne mai muhimmanci a sabunta ka’idoji da matakin karshe na shari’o’in Tokyo watau Tokyo Trials.
Kakakin ya ce, a ranar 3 ga watan Mayun shekarar 1946, biyo bayan tanade-tanaden mika wuya da Japan ta yi ba tare da wani sharadi ba da kuma na kotun hukunta laifukan yakin duniya na II da kasashen kawance suka gabatar, kotun ta fara sauraron shari’a kan laifukan yakin, kuma bisa haduwar manyan kasashe 11 da hujjoji da shaidu masu karfi da aka gabatar, wadannan shari’o’i sun samu sojojin Japan da laifin kaddamar da yaki da take dokokin kasa da kasa da bayyana irin ta’asar da Japanawa suka aika a kasashen Asiya da dama.
An kuma yankewa manyan masu laifi su 25 hukuncin kisa ta hanyar rataya ko zaman gida yari, cikinsu har da Hideki Tojo. Haka kuma an karyata shari’o’i kamar “shari’ar tabbatar da nasara” da “yakin Japan na kare kai” da “dokar gyara hukunce-hukunce.”
A cewar kakakin, shari’o’in na Tokyo, wanda gwaji ne na sanin ya kamata, ya tabbatar da adalci a tarihi. Kuma idan aka hada da shari’o’in Nuremberg, shari’o’in na Tokyo sun kunyata masu ra’ayin danniya da suka aikata laifukan yaki.
Ya ce bai kamata a yi watsi da adalcin da shari’o’in biyu suka tabbatar ba. Haka kuma bai kamata a kalubalanci ikon da suke da shi bisa doka ba. Kuma bai kamata a jirgita odar duniya da suka shimfida bayan yakin ba.
Bugu da kari, ya ce duk yunkurin wani na yin gangancin gyara hukuncin da aka yanke, zai fuskanci turjiyar jama’ar duniya masu kaunar zaman lafiya, tare da sake gurfana gaban kotu. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post