Jam’iyyar APC a Jihar Gombe ta sanar da Dr. Jamilu Shaiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar gwamna bayan sulhu (consensus) domin shiga zaɓen 2027. An cimma wannan matsaya ne a wani taron masu ruwa da tsaki ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya.
Taron ya kuma amince da ‘yan takara na bai ɗaya a matakin sanatoci uku na jihar, kujerun majalisar wakilai shida da kuma kujerun majalisar dokokin jiha guda 24. Mahalarta taron sun haɗa da masu neman takara, da mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyya (EXCO), da dattawan jam’iyya da sauran manyan jiga-jigai.
Wannan mataki ya biyo bayan tuntuɓar juna da gwamna Inuwa Yahaya ya jagoranta, wanda ya haɗa shugabannin jam’iyya, da masu neman takara da kuma wakilan maazaɓu, domin ƙarfafa haɗin kai da rage saɓani a cikin jam’iyyar kafin zaɓen 2027.
Daga cikin waɗanda aka amince da su a matakin sanatoci sun haɗa da Mohammed Ahmadu Deba (Gombe ta tsakiya), da Jerry Damara (Gombe ta Kudu) da kuma Muhammadu Inuwa Yahaya (Gombe tana Arewa).
Haka kuma, an amince da ‘yan takara a kujerun majalisar wakilai daban-daban ciki har da Usman Bello Kumo (Akko), da Inuwa Garba (Yamaltu/Deba), da Fatima Binta Bello (Kaltungo/Shongom).
Jam’iyyar ta bayyana cewa wannan tsari na bai daya na nufin ƙara ƙarfafa haɗin kai, da daidaito da kuma gabatar da tsayayyen tsari na siyasa gabanin babban zaɓen 2027.















Discussion about this post