Ministan tsaron kasar Japan Koizumi Shinjiro, ya yi wasu kalamai a kwanan nan da suka shafi makaman nukiliya. Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a yau Talata 21 ga watan nan cewa, yunkurin gwamnatin Japan na keta wasu muhimman ka’idoji uku na kasar game da hana mallakar makaman nukiliya da sarrafa su da kuma shigar da su cikin kasar, da kuma kalubalantar odar kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu, a bayyane yake. Sabon ra’ayin nuna karfin soja na kasar Japan ya riga ya kunno kai, inda ya zama dole kasa da kasa su yi taka-tsantsan tare kuma da nuna adawa da shi.
Rahotanni sun ruwaito cewa, ministan tsaron kasar Japan, Koizumi Shinjiro, ya bayyana a wani shirin intanet da aka gabatar a ranar 17 ga watan nan cewa, ya kamata kasarsa ta tattauna manufofin da suka shafi makaman nukiliya ba tare da jin tsoro ba, al’amarin da ya jawo hankula a cikin gida da ma sauran kasashen duniya sosai. (Murtala Zhang)













