Shugaban Hukumar Laliga ta ƙasar Spain, Javier Tebas, ya buƙaci shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino, ya yi murabus daga muƙaminsa.
Ya ce yadda Infantino ke tafiyar da harkokin FIFA ya jawo cece-kuce sosai, musamman bayan gasar cin Kofin Duniya da aka kammala.
A wata hira da ya yi da jaridar La Gazzetta dello Sport ta Italiya, Tebas ya bayyana cewa akwai wasu sabbin dokoki da FIFA ta aiwatar a gasar da ba su yi masa daɗi ba.
Daga ciki akwai hutun shan ruwa na minti biyar a kowane rabin wasa, tsawaita hutun rabin lokaci domin kaɗe-kaɗe da raye-raye, da kuma abin da ya kira tsoma bakin FIFA a hukuncin dakatar da wasu ‘yan wasa.
Tebas ya ce, “Lokacin Infantino ya ƙare.”
Ya ƙara da cewa mutane da dama ba su gamsu da yadda shugaban FIFA ke gudanar da hukumar ba.
Ya kuma soki matakin da FIFA ta ɗauka na soke dakatarwar ɗan wasan Amurka, Folarin Balogun, yana mai cewa hakan bai dace ba.
Har ila yau, Tebas ya nuna rashin amincewarsa da ƙara yawan ƙasashen da ke shiga gasar cin Kofin Duniya ba tare da tuntuɓar manyan masu ruwa da tsaki a harkar ƙwallon ƙafa ba.
Duk da wannan, ana sa ran Infantino zai nemi amincewar shugabannin FIFA domin ci gaba da jagorantar hukumar a taron da za a gudanar a watan Maris.














