Cibiyar kasa da kasa ta IMD, mai horar da shugabanni da ’yan kasuwa ta fitar da rahotonta na shekarar 2026 game da karfin takarar kasashen duniya a fannonin shugabanci da tattalin arziki da kasuwanci, inda kasar Sin ta daga zuwa matsayi na 12 a duniya, yayin da yankin musamman na Hong Kong na kasar Sin, ya kai matsayi na 2.
Da yake amsa tambaya game da batun yayin taron manema labarai na yau Laraba, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana cewa, daga zama cibiyar masana’anatu ta duniya zuwa babbar kasuwar duniya, a yanzu kuma mai karfin kirkire-kirkire, karfin Sin na takara na ci gaba da karuwa.
A cewarsa, wannan na da alaka da yanayin dorewar dabaru da kuma ci gaba cikin sauri da ake samu, wanda kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha ke ingizawa. Ya ce yayin da take ba da karin ribar kasuwa ga duniya, kasar Sin na bayar da gudunmuwa ga karuwar ribar kirkire-kirkire.
Bugu da kari, kasar Sin ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen fadada bude kofarta, da ci gaba da jajircewa wajen cin gajiyar sakamakon kirkire-kirkiren fasaha da dukkan kasashe. (Fa’iza Mustapha)














