Lokacin da ake magana kan jam’iyyar da ke mulki a kasar Sin, wato Jam’iyyar Kwaminis ta kasar, ina matukar son kwatancen da wani dan siyasar kasar Kenya ya yi amfani da shi. Ya ce, “Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kamar wani babban itace ne na Kuka, wanda ke da saiwoyi masu girma, da kuma dabarar warkar da kanta.”Lokacin da aka kafa wannan jam’iyyar siyasa a kan wani karamin jirgin ruwan katako a shekarar 1921, da wuya a yi tunanin cewa daga baya za ta jagoranci kasar Sin cikin nasara wajen kama hanyar zamanantarwa mai zaman kanta, yayin da ita kanta ta girma zuwa babbar jam’iyya mai mambobi sama da miliyan 100.
Mene ne sirrin nasarorin da Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta samu? A yau, a bikin murnar cika shekaru 105 da kafa Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da ya gudana a birnin Beijing na kasar, sakatare janar na jam’iyyar, Xi Jinping, ya bayar da amsa.
A jawabin da ya yi a wajen bikin, Xi ya ambaci kyawawan halaye na jam’iyyarsa, kana guda biyu daga cikinsu sun yi daidai da halayen bishiyar Kuka da aka ambata: “Samun cikakken goyon baya daga jama’a, wanda ya tabbatar da tushenta mai karfi” ya yi daidai da “mallakar saiwoyi masu girma,” yayin da “mayar da hankali kan daidaita tsare-tsarenta a-kai-a-kai” ya yi daidai da “dabarar warkar da kanta.”Wadannan abubuwa halaye ne na musamman da Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ke da su. Kuma kamar yadda wani shehun malami dan Najeriya mai suna Charles Olnunaiju ya fada, fasahohin jam’iyyar sun zama abin koyi ga sauran kasashe.
A lokaci guda kuma, burin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, na gina al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga dan adam, yana tabbatar da cewa jam’iyyar za ta kasance mai wanzar da adalci a duniya a ko da yaushe. (Bello Wang)














