Mataimakin firaministan kasar Sin Ding Xuexiang ya ce a shirye Sin take ta hada hannu da dukkan bangarori wajen bunkasa wadatar makamashi da ci gaba mai dorewa a duniya.Ding Xuexiang, wanda kuma mamba ne na kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ya bayyana haka ne jiya Alhamis, lokacin da yake gabatar da jawabi yayin bikin bude taron ministocin makamashi na kasashen kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta Asia da tekun Pasifik (APEC), a birnin Beijing.
Ya ce kasar Sin za ta kare daidaiton kasuwannin makamashi na duniya da bayar da gudunmuwa ga duniya wurin komawa ga amfani da makamashi mai tsafta, da rage fitar da hayakin Carbon, da shiga a dama da ita cikin hadin gwiwar makamashi na kasa da kasa.
Mataimakin firaministan ya kara da cewa, ana ta damawa da kasar Sin cikin hadin gwiwar makamashi mai muhimmanci karkashin tsarin kungiyar APEC, kuma tana inganta bunkasa harkokin da suka shafi makamashi a yankin, tare da bayar da muhimman gudunmuwa wajen kare wadatar makamashi a duniya. (Fa’iza Mustapha)














