Gwamnatin Tarayya ta ce tana shirin fara wani shiri na ƙwarewar daidaita matsayin malaman makarantu 250,000 da ba su da cikakkiyar cancantar aikin koyarwa, domin inganta ilimin yara a faɗin Nijeriya.
Shirin zai mayar da hankali ne wajen ba malaman horo da ƙwarewar da ake buƙata domin su samu damar cika ƙa’idojpin aikin koyarwa na ƙasa.
Matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na magance ƙarancin ƙwararrun malamai da kuma inganta tsarin koyarwa a makarantun ƙasar, musamman ganin muhimmancin malamai wajen inganta sakamakon karatun ɗalibai.
Gwamnatin ta kuma jaddada buƙatar ƙara saka hannun jari a fannin ilimi da bunƙasa ƙwarewar malamai, domin tabbatar da cewa ɗalibai suna samun ingantaccen ilimi daga malamai masu cikakken horo.
Shirin zai shafi malaman da ba su da cikakkiyar cancantar koyarwa, inda ake sa ran horon zai taimaka wajen ɗaga matsayin su zuwa matakin da ya dace da ƙa’idojin aikin koyarwa a Nijeriya.














