• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Tsaro Ta NATO Ba Za Ta Iya Dora Alhakin Rikicin Ukraine Kan Kasar Sin Ba

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
NATO

Jiya Laraba 11 ga wata, taron koli na kungiyar tsaro ta NATO ya bayar da wata sanarwa, wadda ta kaddamar da mummunan suka kan kasar Sin bisa yadda kungiyar ke yin hadin gwiwa da dabarun Amurka na hana ci gaban kasar Sin, inda ta yi karya na cewa Sin ce ke rura wutar rikicin Rasha da Ukraine, wadda ke haifar da kalubale mai tsauri ga tsaron tekun Atlantika.

Yau kusan shekaru biyu da rabi ana gwabza rikici tsakanin Rasha da Ukraine. Mutane da dama sun fahimci cewa, bayan kawo karshen yakin cacar baka, kungiyar tsaro ta NATO ta ci gaba da kara kaimi wajen fadada ayyukanta na gabas karkashin jagorancin kasar Amurka, inda a kullum take danne sararin tsaron kasar Rasha, wanda shi ne asalin tayar da rikicin Rasha da Ukraine.

  • Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO
  • “ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin

Domin kaucewa daukar alhakinta a rikicin Rasha da Ukraine, NATO ta gabatar da wani “karkataccen ra’ayi”, wato neman shafa wa kasar Sin kashin kaji ta hanyar kirkira labaran karya. Amma, hakan ba zai iya boye alhakin dake kan NATO ba.

Kamar yadda aka sani, kasar Sin ba ita ce mai tayar da rikicin Ukraine ba, kuma ba ta cikin rikicin. Babban matsayin kasar Sin game da batun Ukraine, shi ne inganta yin shawarwari cikin lumana da warware rikicin a siyasance, kuma kasar ba ta taba samar da muggan makamai ga kowane bangare dake cikin rikicin ba, kana tana mayar da hankali sosai kan fitar da kayayyakin da ake amfani da su a fannonin aikin soja da na jama’a.

A matsayinta na wanda ya kaddamar da wannan rikicin, ya kamata Amurka da NATO da ke karkashin jagorancinta su daina dora laifin kan kasar Sin, kuma su dauki kwararan matakai don inganta sassaucin halin da ake ciki.

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Kamar yadda kasar Sin ta ce, sai in dukkan manyan kasashen duniya sun taka muhimmiyar rawa maimakon kawo cikas, za a kai ga matakin tsagaita bude wuta da sauri a tsakanin Rasha da Ukraine. (Bilkisu Xin)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Next Post
‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.