ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, December 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Tsaro Ta NATO Ba Za Ta Iya Dora Alhakin Rikicin Ukraine Kan Kasar Sin Ba

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
NATO

Jiya Laraba 11 ga wata, taron koli na kungiyar tsaro ta NATO ya bayar da wata sanarwa, wadda ta kaddamar da mummunan suka kan kasar Sin bisa yadda kungiyar ke yin hadin gwiwa da dabarun Amurka na hana ci gaban kasar Sin, inda ta yi karya na cewa Sin ce ke rura wutar rikicin Rasha da Ukraine, wadda ke haifar da kalubale mai tsauri ga tsaron tekun Atlantika.

Yau kusan shekaru biyu da rabi ana gwabza rikici tsakanin Rasha da Ukraine. Mutane da dama sun fahimci cewa, bayan kawo karshen yakin cacar baka, kungiyar tsaro ta NATO ta ci gaba da kara kaimi wajen fadada ayyukanta na gabas karkashin jagorancin kasar Amurka, inda a kullum take danne sararin tsaron kasar Rasha, wanda shi ne asalin tayar da rikicin Rasha da Ukraine.

  • Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO
  • “ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin

Domin kaucewa daukar alhakinta a rikicin Rasha da Ukraine, NATO ta gabatar da wani “karkataccen ra’ayi”, wato neman shafa wa kasar Sin kashin kaji ta hanyar kirkira labaran karya. Amma, hakan ba zai iya boye alhakin dake kan NATO ba.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda aka sani, kasar Sin ba ita ce mai tayar da rikicin Ukraine ba, kuma ba ta cikin rikicin. Babban matsayin kasar Sin game da batun Ukraine, shi ne inganta yin shawarwari cikin lumana da warware rikicin a siyasance, kuma kasar ba ta taba samar da muggan makamai ga kowane bangare dake cikin rikicin ba, kana tana mayar da hankali sosai kan fitar da kayayyakin da ake amfani da su a fannonin aikin soja da na jama’a.

A matsayinta na wanda ya kaddamar da wannan rikicin, ya kamata Amurka da NATO da ke karkashin jagorancinta su daina dora laifin kan kasar Sin, kuma su dauki kwararan matakai don inganta sassaucin halin da ake ciki.

LABARAI MASU NASABA

UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Taimakawa Amurka Nemo Gawarwakin Sojojinta Da Suka Bace

Kamar yadda kasar Sin ta ce, sai in dukkan manyan kasashen duniya sun taka muhimmiyar rawa maimakon kawo cikas, za a kai ga matakin tsagaita bude wuta da sauri a tsakanin Rasha da Ukraine. (Bilkisu Xin)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya

December 10, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Taimakawa Amurka Nemo Gawarwakin Sojojinta Da Suka Bace
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Taimakawa Amurka Nemo Gawarwakin Sojojinta Da Suka Bace

December 10, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

December 10, 2025
Next Post
‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nijeriya Ta Himmatu Wajen Inganta Tsarin Karatun Allo

Gwamnatin Nijeriya Ta Himmatu Wajen Inganta Tsarin Karatun Allo

December 11, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja

EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja

December 11, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

December 11, 2025
Rikicin PDP Ne Ya Sanya Ni Komawa Jam’iyyar Accord – Adeleke

Rikicin PDP Ne Ya Sanya Ni Komawa Jam’iyyar Accord – Adeleke

December 11, 2025
Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu

Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu

December 11, 2025
Za Mu Yi Hisabi Da Buhari A Gaban Allah — Sheikh El-Zakzaky

Za Mu Yi Hisabi Da Buhari A Gaban Allah — Sheikh El-Zakzaky

December 11, 2025
UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya

UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya

December 10, 2025
hisba

Ƙirƙirar Hisbah Mai Zaman Kanta: Kungiyar Lauyoyi ‘Yan Kano Ta Shigar Da Tinubu Ƙara

December 10, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Taimakawa Amurka Nemo Gawarwakin Sojojinta Da Suka Bace

Sin Na Ci Gaba Da Taimakawa Amurka Nemo Gawarwakin Sojojinta Da Suka Bace

December 10, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

An Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa Na Sin Da Afrika Kan Kare Hakkin Dan Adam

December 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.