Gwamnatin Tarayya, ta sha alwashin tabbatar da inganta tsarin koyar da karatun Allo da yadda ake gudanar da ilimin tsangayu a faɗin ƙasar.
Ministan Ilimi na Nijeriya, Dakta Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan biyo bayan taron ƙaddamar da tsarin inganta koyar da Karatun Allo da ilimin Tsangayu na bai-ɗaya, wanda ya gudana a ranar Litinin din da ta gabata, a Babban Birnin Tarayya Abuja.
- EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja
- Rikicin PDP Ne Ya Sanya Ni Komawa Jam’iyyar Accord – Adeleke
Da yake yi wa manema labarai ƙarin haske dangane da wannan gagarumin sauyi da ma’aikatar ilimin ke ƙoƙarin aiwatarwa, mai taimaka wa Ministan ilimin kan ilimin Almajirai da Tsangayu da da Makarantun Allo, Dakta Balarabe Shehu Kakale, ya ce nan ba da jimawa ba Makarantun Allo za su dinga gogayya da takwarorinsu na Boko da ke faɗin ƙasar.
Kakale, wanda shi ne Barden Tsangayu da Makarantun Allo na Ƙasar Hausa, ya ƙara da cewa manufar samar da tsarin shi ne don ingata rayuwar Almajiran da ke lungu da saƙo na Nijeriya.
A cewar Dakta Kakale, “Kafin a kai ga wannan matsaya, sai da muka karaɗe ɗaukacin shiyyoyin siyasa shida na Nijeriya, inda muka tattauna da masu ruwa da tsaki kamar malamai da sarakuna har ma da ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN), wanda kuma akwai bukatar ganin gwamnatocin jihohi sun kara zage damtse wajen kaiwa ga cikakkiyar nasara”.
Daga bisani ya yaba wa Ministan ilimin ƙasar Dakta Tunji Alausa, da Ministar Kasa a ma’aikatar ilimi, Dakta Suwaiba Ahmed, shugaban hukumar Kula da ilimin Almajirai da yaran da basa zuwa makaranta ta Nijeriya, Dakta Mohammed Sani Idris, har ma jagororin addinai da sarakuna, bisa matakan da suke ɗauka na inganta ilimin Almajirai dama rayuwar yaran da basa zuwa makaranta ta hanyar koyar da su sana’oin hannu wanda zai basu damar dogaro da kansu, a ƙarƙashin shirin.














