Kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa Amurka a kokarin da take yi na nemo gawarwakin jami’anta na sojoji da suka bace a yankin kasar Sin, tun lokacin yakin da Sin ta yi da maharan Japan daga shekarar 1931-1945.
Ma’aikatar tsaron kasar Sin ce ta bayyana haka, inda ta kara da cewa, rundunonin sojojin Sin da na Amurka sun yi taro ta kafar bidiyo game hadin gwiwar bayanai da daftarori na tarihi a yau Laraba, inda suka yi musayar ra’ayi kan hadin gwiwar tare da amincewa da wata kwarya kwaryar shirin hadin gwiwa na shekarar 2026. (Mai fassara: FMM)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT














