Sin da Afrika sun yi taron kara wa juna sani na hadin gwiwa kan kare hakkin dan Adam, yau Laraba a birnin Jinhua na lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin, albarkacin ranar hakkin dan Adam ta duniya.
Taron wanda aka gudanar a jami’ar horar da malamai ta Zhejiang, ta hada masana da malamai sama da 100 daga bangarori daban-daban, inda suka tattauna a fannoni da dama da suka hada da manyan shawarwarin 4 da suka shafi duniya da Sin ta gabatar, da tsarin tafiyar da harkokin kare hakkin dan Adam a duniya, da kuma hadin gwiwar Sin da Afrika a aikace.
Yayin taron, an kaddamar da dandalin musayar ra’ayi da nazarin harkokin kare hakkin dan Adam ta Sin da Afrika a hukumance, yayin da aka kaddamar da cibiyar nazarin harkokin kare hakkin dan Adam ta Sin da Afrika a cibiyar nazarin harkokin Afrika dake jami’ar. (Mai fassara: FMM)














