Rundunar Sojin Nijeriya ta ce tawagar sojojinta da ke yaƙi da ’yan bindiga a Sakkwato, ta kashe ’yan bindiga 11 tare da ƙwato wasu makamai masu yawa.
A wata sanarwa, sojojin suka fitar, sun ce sun samu bayanan sirri, suka shirya tarko, sannan suka yi musayar wuta da ’yan bindigar.
- Za Mu Yi Hisabi Da Buhari A Gaban Allah — Sheikh El-Zakzaky
- Gwamnati Ta Yaƙi Talauci, Rashin Tsaro, ’Yancin Jama’a Don A Hana Aukuwar Juyin Mulki A Nijeriya – Falana
Sun kashe 11 daga cikinsu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.
Sojojin sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda takwas, mujallu guda biyar, da harsashi 26.
An gudanar da aikin ne a kusa da garin Kurawa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Birni, kuma hakan ya daƙile wani harin da ’yan bindigar suka shirya kai wa ƙauyen Tara.
Sojojin sun ce wannan nasara ta daƙile mumunin hari, ta kuma raunana Kungiyar ’yan bindiga a yankin Sabon Birni, wanda ya daɗe yana fama da hare-hare.
Rundunar ta ce sojoji za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a Sakkwato da kewaye.














