Gwamnatin Jihar Neja ta miƙa yara 100 da aka kuɓutar, waɗanda aka sace daga Makarantar Katolika ta St Mary’s da ke Papiri, ga iyayensu bayan shafe makonni biyu a hannun ’yan bindiga.
Harabar makarantar ta cika da iyayensu cikin farin ciki, inda suka jira ganin ’ya’yansu da aka dawo da su daga Minna.
- UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya
- Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi
Kwamishinan ’yansandan jihar ya ce an duba lafiyar yaran, kuma duk suna cikin ƙoshin lafiya.
Wasu iyayen yaran sun ce sun kwana suna jiran wannan rana, kuma ganin ’ya’yansu cikin lafiya ya sanya su farin ciki.
Gwamnatin jihar ta ce tana ci gaba da aiki domin ganin an sako sauran ɗalibai 153 da ma’aikata 12 da ke hannun ’yan bindigar.
Ta kuma yi alƙawarin ƙara tsaro a makarantu domin kare yaran daga irin wannan hari a nan gaba.












