An kama tsohon gwamnan Jihar Anambra kuma tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige, a Abuja.
Yanzu haka yana hannun Hukumar EFCC.
- Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
- Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu
Wannan bayani ya fito ne a daren ranar Laraba ta bakin tsohon mai taimaka masa kan yaɗa labarai, Fred Chukwulobe.
ADVERTISEMENT
Chukwulobe, ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo cewa an yi garkuwa da Ngige.
Ya ce, “Dr. Chris Ngige yana hannun EFCC. Za a yi ƙarin bayani daga baya.”
A kwanakin baya, an samu labari cewa wasu ‘yan bindiga sun kai wa tawagar motocin Ngige hari a Jihar Anambra, amma ba ya cikin ayarin lokacin da lamarin ya faru.














