Ƙungiyar Lauyoyi ‘yan asalin jihar Kano ta maka Shugaba Bola Tinubu da Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa (NSA), Mallam Nuhu Ribadu, a kotu kan shirin samar da wata ƙungiyar Hisbah mai zaman kanta a Kano mai kama da wacce ake da ita a jihar, tana mai gargadin cewa, matakin zai iya barazana ga zaman lafiya da tsaro da ake da shi a jihar.
A cikin takardar da Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Malam Usman Imam Tudun Wazirichi, da Sakatariyarta ta Ƙasa, Rita Benedict, Esq. suka sanya wa hannu, lauyoyin sun yi zargin cewa ɗaukar jami’an ƙirƙirarriyar Hisba mai zaman kanta wani ɓangare ne na siyasa kawai da ka iya wargaza zaman lafiyar jihar Kano.
- Asusun IMF Ya Daga Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Sin
- Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi
Sun yi iƙirarin cewa, shirin da ke da alaƙa da tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, zai iya kawo cikas ga zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista a jihar.
A cewar lauyoyin, rikice-rikicen tsaro na baya-bayan nan a sassan Kano ya nuna a fili, “yunƙurin ƙirƙirar rashin tsaro don samun ribar siyasa.”
Kungiyar ta yi gargadin cewa, samar da wata hukumar Hisbah mai zaman kanta na iya raunana ikon zaɓaɓɓiyar gwamnatin jihar.
Sun kuma yi gargadin cewa, idan ba a dauki matakin gaggawa ba, wannan ci gaban zai iya tura Kano zuwa ga irin rashin tsaro da ake fuskanta a jihohi kamar Borno da Zamfara.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wannan matakin ya biyo bayan fitar da fom din daukar jami’ai 12,000 na hukumar Hisbah mai zaman kanta da ake shirin ƙirƙira a karshen makon da ya gabata.
An ruwaito cewa Baffa Dan Agundi, tsohon Manajan Darakta na Hukumar Kula da Zirga-zirgar Hanyoyi ta Kano (KAROTA), da tsohon Kwamandan Hisbah, Sheikh Harun Ibn Sina ne suka gudanar da rajistar jami’an a madadin Gidauniyar Ganduje.














