Hukumar kula da cinikayya da ci gaba ta MDD (UNCTAD), da cibiyar kula da hadin gwiwar cinikayya da tattalin arziki ta kasa da kasa ta ma’aikatar kula da cinikayya ta kasar Sin, sun fitar da rahoto game da harkokin ci gaba da na cinikayya a duniya na 2025, yau Laraba a birnin Beijing.
Rahoton ya bayyana cewa, duk da tarin sabbin sauye-sauye da rashin tabbas a harkokin cinikayya na duniya, sama da kaso 70 na hada-hadar cinikayya na kiyaye ka’idojin hukumar kula da cinikayya ta duniya WTO. Baya ga haka, kasar Sin tana daukaka tsarin cinikayya tsakanin bangarori daban-daban da samar da tabbaci da kwanciyar hankali ga duniya, kuma ta kasance mai dagorantar ci gaban kasashe masu tasowa.
Rahoton ya kuma bayyana cewa, sama da kaso 90 na harkokin cinikayya a duniya sun dogara da tsare-tsaren kudi na duniya, don haka gyare-gyare a bangaren tafiyar da harkokin kudi na duniya zai kasance muhimmin abun da za a mayar da hankali kan sa a mataki na gaba. (Mai fassara: FMM)














