Shugaban mabiya Shi’a a Nijeriya, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, ya ce zai bari Allah Ya yi masa hukunci tsakaninsa da tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, kan abin da ya faru da mambobin ƙungiyarsa a Zariya a shekarar 2015.
Rikicin ya fara ne lokacin da mambobin ƙungiyar suka tare wa tsohon Hafsan Soji, Laftanar Janar Tukur Buratai, hanya.
- UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya
- Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi
Abin da ya fara ne da rashin jituwa sannan ya rikiɗe zuwa babban rikici, inda sojoji suka buɗe wuta kan mabiyan ƙungiyar.
Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da rahoton kwamitin bincike na Jihar Kaduna sun tabbatar da cewa an kashe ɗaruruwan mambobin IMN kuma an binne su a asirce cikin daren da lamarin ya faru.
Daga baya an kama Sheikh Zakzaky da matarsa, aka tsare su har tsawon shekaru shida, kafin kotu ta wanke su a 2021.
A yayin cika shekaru 10 da faruwar lamarin, Zakzaky, ya zargi gwamnatin Buhari da kin ɗaukar alhaki, duk da rahoton binciken da kwamitin ya kammala tun 2016.
Ya ce har yanzu gwamnatin yanzu ba ta ɗauki matakin da ta yi alƙawari ba, duk da cewa ta ce za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.
Ya ce: “Sun ce za su magance batun, amma shiru kake ji tun wancan lokacin.”
Da aka tambaye shi ko ya yafe wa Buhari, Zakzaky, ya ce ya bar komai a wajen Allah, kuma zai yi hisabi da shi a Ranar Alƙiyama.
Ya ce: “A ranar Alƙiyama za mu haɗu. Rayuwar Buhari ta ƙare.”
Zakzaky, ya ƙara da cewa harin da aka kai a 2015 bai karya ƙungiyarsu ta IMN ba, maimakon haka ya ƙara girman sunan ƙungiyar tare da yin fice a duniya.
Ya bayyana cewa sun kai ƙarar lamarin zuwa kotun ƙasa da ƙasa domin neman adalci, kuma a shirye suke su tattauna da gwamnati a ko da yaushe.














