ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Yi Hisabi Da Buhari A Gaban Allah — Sheikh El-Zakzaky

by Sadiq
6 months ago
Hisabi

Shugaban mabiya Shi’a a Nijeriya, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, ya ce zai bari Allah Ya yi masa hukunci tsakaninsa da tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, kan abin da ya faru da mambobin ƙungiyarsa a Zariya a shekarar 2015.

Rikicin ya fara ne lokacin da mambobin ƙungiyar suka tare wa tsohon Hafsan Soji, Laftanar Janar Tukur Buratai, hanya.

  • UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi

Abin da ya fara ne da rashin jituwa sannan ya rikiɗe zuwa babban rikici, inda sojoji suka buɗe wuta kan mabiyan ƙungiyar.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da rahoton kwamitin bincike na Jihar Kaduna sun tabbatar da cewa an kashe ɗaruruwan mambobin IMN kuma an binne su a asirce cikin daren da lamarin ya faru.

Daga baya an kama Sheikh Zakzaky da matarsa, aka tsare su har tsawon shekaru shida, kafin kotu ta wanke su a 2021.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A yayin cika shekaru 10 da faruwar lamarin, Zakzaky, ya zargi gwamnatin Buhari da kin ɗaukar alhaki, duk da rahoton binciken da kwamitin ya kammala tun 2016.

Ya ce har yanzu gwamnatin yanzu ba ta ɗauki matakin da ta yi alƙawari ba, duk da cewa ta ce za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.

Ya ce: “Sun ce za su magance batun, amma shiru kake ji tun wancan lokacin.”

Da aka tambaye shi ko ya yafe wa Buhari, Zakzaky, ya ce ya bar komai a wajen Allah, kuma zai yi hisabi da shi a Ranar Alƙiyama.

Ya ce: “A ranar Alƙiyama za mu haɗu. Rayuwar Buhari ta ƙare.”

Zakzaky, ya ƙara da cewa harin da aka kai a 2015 bai karya ƙungiyarsu ta IMN ba, maimakon haka ya ƙara girman sunan ƙungiyar tare da yin fice a duniya.

Ya bayyana cewa sun kai ƙarar lamarin zuwa kotun ƙasa da ƙasa domin neman adalci, kuma a shirye suke su tattauna da gwamnati a ko da yaushe.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu

Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.