ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Yi Hisabi Da Buhari A Gaban Allah — Sheikh El-Zakzaky

by Sadiq
7 months ago
Hisabi

Shugaban mabiya Shi’a a Nijeriya, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, ya ce zai bari Allah Ya yi masa hukunci tsakaninsa da tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, kan abin da ya faru da mambobin ƙungiyarsa a Zariya a shekarar 2015.

Rikicin ya fara ne lokacin da mambobin ƙungiyar suka tare wa tsohon Hafsan Soji, Laftanar Janar Tukur Buratai, hanya.

  • UNCTAD: Sin Na Daukaka Tsarin Cinikayya Tsakanin Bangarori Daban Daban Da Samar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Ba Ni Da Shirin Komawa PRP – Gwamnan Bauchi

Abin da ya fara ne da rashin jituwa sannan ya rikiɗe zuwa babban rikici, inda sojoji suka buɗe wuta kan mabiyan ƙungiyar.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da rahoton kwamitin bincike na Jihar Kaduna sun tabbatar da cewa an kashe ɗaruruwan mambobin IMN kuma an binne su a asirce cikin daren da lamarin ya faru.

Daga baya an kama Sheikh Zakzaky da matarsa, aka tsare su har tsawon shekaru shida, kafin kotu ta wanke su a 2021.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A yayin cika shekaru 10 da faruwar lamarin, Zakzaky, ya zargi gwamnatin Buhari da kin ɗaukar alhaki, duk da rahoton binciken da kwamitin ya kammala tun 2016.

Ya ce har yanzu gwamnatin yanzu ba ta ɗauki matakin da ta yi alƙawari ba, duk da cewa ta ce za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.

Ya ce: “Sun ce za su magance batun, amma shiru kake ji tun wancan lokacin.”

Da aka tambaye shi ko ya yafe wa Buhari, Zakzaky, ya ce ya bar komai a wajen Allah, kuma zai yi hisabi da shi a Ranar Alƙiyama.

Ya ce: “A ranar Alƙiyama za mu haɗu. Rayuwar Buhari ta ƙare.”

Zakzaky, ya ƙara da cewa harin da aka kai a 2015 bai karya ƙungiyarsu ta IMN ba, maimakon haka ya ƙara girman sunan ƙungiyar tare da yin fice a duniya.

Ya bayyana cewa sun kai ƙarar lamarin zuwa kotun ƙasa da ƙasa domin neman adalci, kuma a shirye suke su tattauna da gwamnati a ko da yaushe.

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu

Gwamnatin Neja Ta Miƙa Yara 100 Da Aka Ceto Ga Iyayensu

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.