Dangane da sanarwar hadin gwiwa da Amurka, da Philippines, da Austiraliya da Japan, da wasu sauran kasashe suka fitar a ranar 12 ga watan nan, don tunawa da cika shekaru goma da fitar da “hukuncin tekun kudancin Sin”, wasu manyan ‘yan siyasa da masana daga kasashe daban-daban, sun shaida wa ’yan jarida na kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, suna goyon bayan kasar Sin a fannin kare ikon mallakar yankunanta dangane da tsibiran tekun kudancin Sin da sauran hakkokin kasar na teku.
Kazalika, sun bayyana “hukuncin” da cewa ya sabawa ka’ida, kuma hukuncin banza ne. Ban da wannan kuma, yadda wasu ‘yan kasashen ketare ke amfani da cika shekaru goma da fitar da “hukuncin” don tayar da hankali, zai tsananta yanayin da ake ciki a yankin.
Babban editan sashen ketare na jaridar “The Guardian” ta Tanzaniya Benjamin Mgana, ya bayyana cewa, ya kamata al’ummun kasa da kasa su mutunta kokarin da Sin da kasashen ASEAN ke yi na ciyar da shawarwarin “ka’idojin ayyukan da za a gudanar a tekun kudancin Sin”. Ya kuma ce, “Ga manyan kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka, muna mai da hankali kan yanayin neman samun ci gaba cikin lumana. A matsayin muhimmiyar hanyar sufuri ta kasa da kasa, da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin Sin, hakan yana da amfani ga al’ummar kasa da kasa baki daya.”
Farfesa Sylvain Kassia Gueu na makarantar kasuwanci ta Abidjan na Cote d’Ivoire ya ce, Sin tana taka rawar gani wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin Sin, kuma tana nacewa ga gudanar da tattaunawa da shawarwari da tuntuba a matsayin muhimman hanyoyin magance rigingimu, tare da dukufa kan inganta zaman lafiya da hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa. (Amina Xu)














