Wata babbar Kotun da ke Gombe ta bayar da umarnin tsare shugaban makarantar Destiny Treasure International School da ke unguwar Arawa da kuma wani malami a gidan gyaran hali mai matsakaicin tsaro, bisa zargin lalata da wata ɗaliba mai shekara shida.
A cikin rahoton da Daily Trust ta sanar, ta bayyana cewa, Alƙaliyar kotun, Hamaira Bema Demba, ta ba da umarnin tsare waɗanda ake tuhuma har zuwa ranar da za a yanke hukunci a shari’ar.
A cewar masu gabatar da ƙara, a watan Yulin 2026 wani malamin aji mai suna Eleazer Yila ya yi lalata da ɗalibar mai shekara shida.
Masu gabatar da ƙarar sun shaida wa kotu cewa lamarin ya fito fili ne bayan yarinyar ta sanarwa mahaifiyarta, Saratu Emmanuel, abin da ya faru.
Haka kuma, an zargi shugaban makarantar, Nasiru Barau Manun, da ƙoƙarin rufe lamarin maimakon ya kai rahoto ga hukumomin da abin ya shafa.
Mai gabatar da ƙara na gwamnati, Manir Mohammed Sambo, tare da lauya Nafi’u Abubakar, sun bayyana wa kotu cewa laifukan sun saɓa da Sashe na 285 da na 167 na Dokar Penal Code.
Bayan an karanta musu tuhume-tuhumen tare da yi musu bayani, duka waɗanda ake tuhuma sun amsa laifinsu.
Daga nan ne kotun ta bayar da umarnin tsare su a gidan gyaran hali mai matsakaicin tsaro, sannan ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 28 ga Yulin 2026, domin yanke hukunci.














