Uwargidan Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa Nijeriya za ta zama ƙasa mai cike da zaman lafiya, albarka da wadata.
Haka kuma, ta ce Nijeriya ba za ta kasance ƙasa marar albarka ba, sai dai ƙasa mai yalwa da ci gaba.
Uwargidan Shugaban Ƙasar ta bayyana hakan ne a ranar Talata yayin ƙaddamar da aikin cibiyar rarraba ruwan sha zuwa garin Bwari Satellite Town a Babban Birnin Tarayya (FCT).
ADVERTISEMENT
Aikin na daga cikin shirye-shiryen da aka tanada domin bikin cika shekaru uku da Bola Ahmed Tinubu ya yi a kan mulkin Nijeriya.














