Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya jagoranci taron liyafar maraba da sabuwar shekara ta 2026 na ma’aikatar harkokin wajen, a birnin Beijing, a ranar Alhamis.
Yayin da yake jawabi a taron liyafar, Wang ya ce duk da kalubalen da ake samu a dangantakar kasa da kasa, Sin ta ci gaba da bin turba mai kyau a sha’anin diflomasiyyarta cikin shekarar da ta gabata. Musamman, shawarar inganta jagorancin duniya da Sin ta gabatar ta haskaka hanyar da ta ce duniya ta bi a wani muhimmin lokaci na sauye-sauyen tsarin duniya.
Ya jaddada cewa duk yadda duniya ta sauya, matsayar Sin na kare adalci da gaskiya a harkokin duniya tana nan daram, kuma jajircewarta wajen gina al’umma mai makoma daya ga dan Adam ba ta yi rauni ba.
A nasa bangaren, Martin Mpana, shugaban kungiyar jakadun kasashen waje a kasar Sin kuma jakadan Kamaru a Sin, ya ce kasashen duniya suna da aniyar yin aiki tare da Sin domin karfafa fahimtar juna, zurfafa abota da karfafa hadin gwiwa, da nufin kare adalci a duniya da kuma karfafa samun ci gaba na bai-daya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post