Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Ƙasa (NCDC) ta tabbatar da samun sabbin mutane da suka kamu cutar zazzaɓin Lassa su 31 a jihohin Ondo, Taraba, Benue da Bauchi.
Jimillar adadin waɗanda suka kamu da cutar a shekarar 2026 ya kai 922, yayin da adadin waɗanda suka mutu ya karu zuwa 221.
NCDC ta ce jihohi 23 sun tabbatar da ɓullar cutar a bana.
Mafi yawan waɗanda suka kamu da cutar sun fito daga jihohin Bauchi, Ondo, Taraba, Benue da Edo.
Hukumar ta buƙaci ‘yan Nijeriya su tsaftace muhalli, su hana ɓeraye shiga gidajensu da wuraren adana abinci.
Sannan su garzaya asibiti idan sun fara ganin alamomin cutar kamar zazzaɓi, ciwon kai ko zubar jini ba tare da wani dalili ba.













