ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Biyafara

Kafin dai a kai ga tsunduma yakin basasa na Biyafara, za mu iya cewa komai yana da dalili. Al’amarin yakin ya samo asali ne bayan juyin mulki na farko da aka yi a jamhuriyya ta daya, ranar 15 ga watan Janairu 1966, lokacin ana da shiyya uku da suka hada da sashen Arewa, sashen Yamma da kuma sashen Gabas.

An kashe manyan shugabannin siyasa na Arewa da suka hada da Firayim Minista na farko, Sa Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyar Arewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato da wasu manyan jami’an sojoji ‘yan Arewa kamar Birgediya Zakari Maimalari, da Firimiyan Sashen Yammacin Nijeriya Samuel Ladoke Akintola da Birgediya Ademulegun.

  • Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa
  • Yawaitar Juyin Mulki A Afirka Na Nuna Matasa Suna Neman Masu ‘Yanci – Obasanjo

Wannan ya sa wasu sojoji musamman na Arewa suka harzuka tare da kitsa juyin mulki na biyu a ranar 29 ga watan Yuli, 1966, lamarin da bai yi wa musamman ‘yan kabilar Ibo dadi ba, saboda wanda aka tuntsurar janar Aguyi Ironsi, dan asalin yankinsu ne.

ADVERTISEMENT

Sannu a hankali har aka kai ga fara yakin duk da kafin a kai ga hakan akwai rigingimun siyasar da suka sa aka kirkiro wani sashe da ya kasance na hudu a lokacin da ake kira ‘Midwest’ wanda a lokacin Nijeriya ta kasance tana da sassa hudu ke nan, sai dai duk da hakan ba a sami wani al’amari na kwantar da wutar ba har dai abin ya kai ga fara yakin Basasar Nijeriya da ya dauki tsawon shekara biyu da wata shida da mako daya da kwana biyu ana yi, watau daga 6 ga Yuli, 1967 zuwa 15 ga Janairu 1970.

A tsawon lokacin da aka yi ana yakin akwai abinda aka yi da ake kira da suna ‘a ware’ da ke nufin ‘yan kabilar Ibo ko kuma Inyamrai da suke da zama a Arewacin Nijeriya suna gudanar da harkokinsu su koma gida kamar yadda su ma ‘yan Arewacin Nijeriya masu harkokinsu a can suka dawo gida.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Daga cikin manyan hafsoshin sojin Nijeriya da suka fafata yakin basasar bisa jagorancin shugaban kasa na wancan lokacin, Janar Yakubu Gowon, akwai Janar Hassan Usman Katsina, Muhammed Shuwa, Benjamin Adekunle, Theophilus Yakubu Danjuma, Shehu Musa ‘Yar’adua, Murtala Muhammed, Olusegun Obasanjo, Muhammadu Buhari, Ibrahim Badamasi Babangida, sai Sani Abacha da Abdulsalam Abubakar, bangaren sojan Nijeriya kenan.

Daga bangaren sojoji masu son ballewa daga Nijeriya a karkashin jagorancin Cief Odumegwu Ojukwu, akwai Philip Effiong, Albert Okwonkwo, Bictor Banjo, Ogbugo Kalu, Joseph Achuzie, Timothy Onwuatiegwue,da kuma Humphrey Chukwuka.

Daga cikin manyan hafsoshin da suka yi yakin dai, akwai wadanda suka yi nasarar zama shugabannin kasa, wasu a mulkin soja kawai, wasu kuma sun yi a mulkin soja da farar hula kamar Olusegun Obasajo da Muhammadu Buhari.

Masu mulkin soja kawai kuma, akwai Murtala Ramat Muhammed, Ibrahim Badamasi Babangida, Sani Abacha, Abdulsalam Abubakar, sai Shehu Musa ‘Yar’adua da ya kasance mataimakin shugaban kasa a mulkin soja na Olusegun Obasanjo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Japan

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.