• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Biyafara

Kafin dai a kai ga tsunduma yakin basasa na Biyafara, za mu iya cewa komai yana da dalili. Al’amarin yakin ya samo asali ne bayan juyin mulki na farko da aka yi a jamhuriyya ta daya, ranar 15 ga watan Janairu 1966, lokacin ana da shiyya uku da suka hada da sashen Arewa, sashen Yamma da kuma sashen Gabas.

An kashe manyan shugabannin siyasa na Arewa da suka hada da Firayim Minista na farko, Sa Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyar Arewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato da wasu manyan jami’an sojoji ‘yan Arewa kamar Birgediya Zakari Maimalari, da Firimiyan Sashen Yammacin Nijeriya Samuel Ladoke Akintola da Birgediya Ademulegun.

  • Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa
  • Yawaitar Juyin Mulki A Afirka Na Nuna Matasa Suna Neman Masu ‘Yanci – Obasanjo

Wannan ya sa wasu sojoji musamman na Arewa suka harzuka tare da kitsa juyin mulki na biyu a ranar 29 ga watan Yuli, 1966, lamarin da bai yi wa musamman ‘yan kabilar Ibo dadi ba, saboda wanda aka tuntsurar janar Aguyi Ironsi, dan asalin yankinsu ne.

Sannu a hankali har aka kai ga fara yakin duk da kafin a kai ga hakan akwai rigingimun siyasar da suka sa aka kirkiro wani sashe da ya kasance na hudu a lokacin da ake kira ‘Midwest’ wanda a lokacin Nijeriya ta kasance tana da sassa hudu ke nan, sai dai duk da hakan ba a sami wani al’amari na kwantar da wutar ba har dai abin ya kai ga fara yakin Basasar Nijeriya da ya dauki tsawon shekara biyu da wata shida da mako daya da kwana biyu ana yi, watau daga 6 ga Yuli, 1967 zuwa 15 ga Janairu 1970.

A tsawon lokacin da aka yi ana yakin akwai abinda aka yi da ake kira da suna ‘a ware’ da ke nufin ‘yan kabilar Ibo ko kuma Inyamrai da suke da zama a Arewacin Nijeriya suna gudanar da harkokinsu su koma gida kamar yadda su ma ‘yan Arewacin Nijeriya masu harkokinsu a can suka dawo gida.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Daga cikin manyan hafsoshin sojin Nijeriya da suka fafata yakin basasar bisa jagorancin shugaban kasa na wancan lokacin, Janar Yakubu Gowon, akwai Janar Hassan Usman Katsina, Muhammed Shuwa, Benjamin Adekunle, Theophilus Yakubu Danjuma, Shehu Musa ‘Yar’adua, Murtala Muhammed, Olusegun Obasanjo, Muhammadu Buhari, Ibrahim Badamasi Babangida, sai Sani Abacha da Abdulsalam Abubakar, bangaren sojan Nijeriya kenan.

Daga bangaren sojoji masu son ballewa daga Nijeriya a karkashin jagorancin Cief Odumegwu Ojukwu, akwai Philip Effiong, Albert Okwonkwo, Bictor Banjo, Ogbugo Kalu, Joseph Achuzie, Timothy Onwuatiegwue,da kuma Humphrey Chukwuka.

Daga cikin manyan hafsoshin da suka yi yakin dai, akwai wadanda suka yi nasarar zama shugabannin kasa, wasu a mulkin soja kawai, wasu kuma sun yi a mulkin soja da farar hula kamar Olusegun Obasajo da Muhammadu Buhari.

Masu mulkin soja kawai kuma, akwai Murtala Ramat Muhammed, Ibrahim Badamasi Babangida, Sani Abacha, Abdulsalam Abubakar, sai Shehu Musa ‘Yar’adua da ya kasance mataimakin shugaban kasa a mulkin soja na Olusegun Obasanjo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Japan

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.