• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Rahotonni
0
Biyafara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafin dai a kai ga tsunduma yakin basasa na Biyafara, za mu iya cewa komai yana da dalili. Al’amarin yakin ya samo asali ne bayan juyin mulki na farko da aka yi a jamhuriyya ta daya, ranar 15 ga watan Janairu 1966, lokacin ana da shiyya uku da suka hada da sashen Arewa, sashen Yamma da kuma sashen Gabas.

An kashe manyan shugabannin siyasa na Arewa da suka hada da Firayim Minista na farko, Sa Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyar Arewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato da wasu manyan jami’an sojoji ‘yan Arewa kamar Birgediya Zakari Maimalari, da Firimiyan Sashen Yammacin Nijeriya Samuel Ladoke Akintola da Birgediya Ademulegun.

  • Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa
  • Yawaitar Juyin Mulki A Afirka Na Nuna Matasa Suna Neman Masu ‘Yanci – Obasanjo

Wannan ya sa wasu sojoji musamman na Arewa suka harzuka tare da kitsa juyin mulki na biyu a ranar 29 ga watan Yuli, 1966, lamarin da bai yi wa musamman ‘yan kabilar Ibo dadi ba, saboda wanda aka tuntsurar janar Aguyi Ironsi, dan asalin yankinsu ne.

Sannu a hankali har aka kai ga fara yakin duk da kafin a kai ga hakan akwai rigingimun siyasar da suka sa aka kirkiro wani sashe da ya kasance na hudu a lokacin da ake kira ‘Midwest’ wanda a lokacin Nijeriya ta kasance tana da sassa hudu ke nan, sai dai duk da hakan ba a sami wani al’amari na kwantar da wutar ba har dai abin ya kai ga fara yakin Basasar Nijeriya da ya dauki tsawon shekara biyu da wata shida da mako daya da kwana biyu ana yi, watau daga 6 ga Yuli, 1967 zuwa 15 ga Janairu 1970.

A tsawon lokacin da aka yi ana yakin akwai abinda aka yi da ake kira da suna ‘a ware’ da ke nufin ‘yan kabilar Ibo ko kuma Inyamrai da suke da zama a Arewacin Nijeriya suna gudanar da harkokinsu su koma gida kamar yadda su ma ‘yan Arewacin Nijeriya masu harkokinsu a can suka dawo gida.

Labarai Masu Nasaba

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Daga cikin manyan hafsoshin sojin Nijeriya da suka fafata yakin basasar bisa jagorancin shugaban kasa na wancan lokacin, Janar Yakubu Gowon, akwai Janar Hassan Usman Katsina, Muhammed Shuwa, Benjamin Adekunle, Theophilus Yakubu Danjuma, Shehu Musa ‘Yar’adua, Murtala Muhammed, Olusegun Obasanjo, Muhammadu Buhari, Ibrahim Badamasi Babangida, sai Sani Abacha da Abdulsalam Abubakar, bangaren sojan Nijeriya kenan.

Daga bangaren sojoji masu son ballewa daga Nijeriya a karkashin jagorancin Cief Odumegwu Ojukwu, akwai Philip Effiong, Albert Okwonkwo, Bictor Banjo, Ogbugo Kalu, Joseph Achuzie, Timothy Onwuatiegwue,da kuma Humphrey Chukwuka.

Daga cikin manyan hafsoshin da suka yi yakin dai, akwai wadanda suka yi nasarar zama shugabannin kasa, wasu a mulkin soja kawai, wasu kuma sun yi a mulkin soja da farar hula kamar Olusegun Obasajo da Muhammadu Buhari.

Masu mulkin soja kawai kuma, akwai Murtala Ramat Muhammed, Ibrahim Badamasi Babangida, Sani Abacha, Abdulsalam Abubakar, sai Shehu Musa ‘Yar’adua da ya kasance mataimakin shugaban kasa a mulkin soja na Olusegun Obasanjo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiafraJuyin Mulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashford Ya Yi Hatsarin Mota A Hanyarsa Ta Zuwa Gida Bayan Tashi Daga Wasansu Da Burnley

Next Post

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

Related

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

3 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

3 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 week ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

2 months ago
Next Post
Japan

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.