• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Rahotonni
0
Biyafara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafin dai a kai ga tsunduma yakin basasa na Biyafara, za mu iya cewa komai yana da dalili. Al’amarin yakin ya samo asali ne bayan juyin mulki na farko da aka yi a jamhuriyya ta daya, ranar 15 ga watan Janairu 1966, lokacin ana da shiyya uku da suka hada da sashen Arewa, sashen Yamma da kuma sashen Gabas.

An kashe manyan shugabannin siyasa na Arewa da suka hada da Firayim Minista na farko, Sa Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyar Arewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato da wasu manyan jami’an sojoji ‘yan Arewa kamar Birgediya Zakari Maimalari, da Firimiyan Sashen Yammacin Nijeriya Samuel Ladoke Akintola da Birgediya Ademulegun.

  • Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa
  • Yawaitar Juyin Mulki A Afirka Na Nuna Matasa Suna Neman Masu ‘Yanci – Obasanjo

Wannan ya sa wasu sojoji musamman na Arewa suka harzuka tare da kitsa juyin mulki na biyu a ranar 29 ga watan Yuli, 1966, lamarin da bai yi wa musamman ‘yan kabilar Ibo dadi ba, saboda wanda aka tuntsurar janar Aguyi Ironsi, dan asalin yankinsu ne.

Sannu a hankali har aka kai ga fara yakin duk da kafin a kai ga hakan akwai rigingimun siyasar da suka sa aka kirkiro wani sashe da ya kasance na hudu a lokacin da ake kira ‘Midwest’ wanda a lokacin Nijeriya ta kasance tana da sassa hudu ke nan, sai dai duk da hakan ba a sami wani al’amari na kwantar da wutar ba har dai abin ya kai ga fara yakin Basasar Nijeriya da ya dauki tsawon shekara biyu da wata shida da mako daya da kwana biyu ana yi, watau daga 6 ga Yuli, 1967 zuwa 15 ga Janairu 1970.

A tsawon lokacin da aka yi ana yakin akwai abinda aka yi da ake kira da suna ‘a ware’ da ke nufin ‘yan kabilar Ibo ko kuma Inyamrai da suke da zama a Arewacin Nijeriya suna gudanar da harkokinsu su koma gida kamar yadda su ma ‘yan Arewacin Nijeriya masu harkokinsu a can suka dawo gida.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Daga cikin manyan hafsoshin sojin Nijeriya da suka fafata yakin basasar bisa jagorancin shugaban kasa na wancan lokacin, Janar Yakubu Gowon, akwai Janar Hassan Usman Katsina, Muhammed Shuwa, Benjamin Adekunle, Theophilus Yakubu Danjuma, Shehu Musa ‘Yar’adua, Murtala Muhammed, Olusegun Obasanjo, Muhammadu Buhari, Ibrahim Badamasi Babangida, sai Sani Abacha da Abdulsalam Abubakar, bangaren sojan Nijeriya kenan.

Daga bangaren sojoji masu son ballewa daga Nijeriya a karkashin jagorancin Cief Odumegwu Ojukwu, akwai Philip Effiong, Albert Okwonkwo, Bictor Banjo, Ogbugo Kalu, Joseph Achuzie, Timothy Onwuatiegwue,da kuma Humphrey Chukwuka.

Daga cikin manyan hafsoshin da suka yi yakin dai, akwai wadanda suka yi nasarar zama shugabannin kasa, wasu a mulkin soja kawai, wasu kuma sun yi a mulkin soja da farar hula kamar Olusegun Obasajo da Muhammadu Buhari.

Masu mulkin soja kawai kuma, akwai Murtala Ramat Muhammed, Ibrahim Badamasi Babangida, Sani Abacha, Abdulsalam Abubakar, sai Shehu Musa ‘Yar’adua da ya kasance mataimakin shugaban kasa a mulkin soja na Olusegun Obasanjo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiafraJuyin Mulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashford Ya Yi Hatsarin Mota A Hanyarsa Ta Zuwa Gida Bayan Tashi Daga Wasansu Da Burnley

Next Post

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 hours ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

4 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

5 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

7 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Japan

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.