ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Biyafara

Kafin dai a kai ga tsunduma yakin basasa na Biyafara, za mu iya cewa komai yana da dalili. Al’amarin yakin ya samo asali ne bayan juyin mulki na farko da aka yi a jamhuriyya ta daya, ranar 15 ga watan Janairu 1966, lokacin ana da shiyya uku da suka hada da sashen Arewa, sashen Yamma da kuma sashen Gabas.

An kashe manyan shugabannin siyasa na Arewa da suka hada da Firayim Minista na farko, Sa Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyar Arewa, Sa Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato da wasu manyan jami’an sojoji ‘yan Arewa kamar Birgediya Zakari Maimalari, da Firimiyan Sashen Yammacin Nijeriya Samuel Ladoke Akintola da Birgediya Ademulegun.

  • Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa
  • Yawaitar Juyin Mulki A Afirka Na Nuna Matasa Suna Neman Masu ‘Yanci – Obasanjo

Wannan ya sa wasu sojoji musamman na Arewa suka harzuka tare da kitsa juyin mulki na biyu a ranar 29 ga watan Yuli, 1966, lamarin da bai yi wa musamman ‘yan kabilar Ibo dadi ba, saboda wanda aka tuntsurar janar Aguyi Ironsi, dan asalin yankinsu ne.

ADVERTISEMENT

Sannu a hankali har aka kai ga fara yakin duk da kafin a kai ga hakan akwai rigingimun siyasar da suka sa aka kirkiro wani sashe da ya kasance na hudu a lokacin da ake kira ‘Midwest’ wanda a lokacin Nijeriya ta kasance tana da sassa hudu ke nan, sai dai duk da hakan ba a sami wani al’amari na kwantar da wutar ba har dai abin ya kai ga fara yakin Basasar Nijeriya da ya dauki tsawon shekara biyu da wata shida da mako daya da kwana biyu ana yi, watau daga 6 ga Yuli, 1967 zuwa 15 ga Janairu 1970.

A tsawon lokacin da aka yi ana yakin akwai abinda aka yi da ake kira da suna ‘a ware’ da ke nufin ‘yan kabilar Ibo ko kuma Inyamrai da suke da zama a Arewacin Nijeriya suna gudanar da harkokinsu su koma gida kamar yadda su ma ‘yan Arewacin Nijeriya masu harkokinsu a can suka dawo gida.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Daga cikin manyan hafsoshin sojin Nijeriya da suka fafata yakin basasar bisa jagorancin shugaban kasa na wancan lokacin, Janar Yakubu Gowon, akwai Janar Hassan Usman Katsina, Muhammed Shuwa, Benjamin Adekunle, Theophilus Yakubu Danjuma, Shehu Musa ‘Yar’adua, Murtala Muhammed, Olusegun Obasanjo, Muhammadu Buhari, Ibrahim Badamasi Babangida, sai Sani Abacha da Abdulsalam Abubakar, bangaren sojan Nijeriya kenan.

Daga bangaren sojoji masu son ballewa daga Nijeriya a karkashin jagorancin Cief Odumegwu Ojukwu, akwai Philip Effiong, Albert Okwonkwo, Bictor Banjo, Ogbugo Kalu, Joseph Achuzie, Timothy Onwuatiegwue,da kuma Humphrey Chukwuka.

Daga cikin manyan hafsoshin da suka yi yakin dai, akwai wadanda suka yi nasarar zama shugabannin kasa, wasu a mulkin soja kawai, wasu kuma sun yi a mulkin soja da farar hula kamar Olusegun Obasajo da Muhammadu Buhari.

Masu mulkin soja kawai kuma, akwai Murtala Ramat Muhammed, Ibrahim Badamasi Babangida, Sani Abacha, Abdulsalam Abubakar, sai Shehu Musa ‘Yar’adua da ya kasance mataimakin shugaban kasa a mulkin soja na Olusegun Obasanjo.

Biyafara
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Biyafara
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Biyafara
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Japan

Dagwalon Nukiliyar Japan: Kar Duniya Ta Rungume Hannu Kilu Ta Ja Bau

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.