A yau Talata 10 ga wannan wata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana a gun taron manema labaru cewa, Sin ta nuna kulawa sosai kan halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya. Manzon musamman kan batun yankin Gabas ta Tsakiya na gwamnatin kasar Sin Zhai Jun yana ziyara a yankin, kuma an riga an gabatar da labari game da ziyararsa a kasar Saudiyya a shafin internet na ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin.
Game da ra’ayin shugaban kasar Amurka Donald Trump kan sabon jagoran koli na kasar Iran, Guo Jiakun ya bayyana cewa, an yi zaben sabon jagoran koli na kasar Iran bisa kundin tsarin mulkin kasar. Bai kamata a tsoma baki a harkokin cikin gida na wata kasa ba, kuma wannan ce ka’idar raya huldar dake tsakanin kasa da kasa.
Ban da wannan kuma, Guo Jiakun ya kara da cewa, yankin mashigin Hormuz da sassan dake yankin, na da matukar muhimmanci ga sassan kasa da kasa ta fuskar safarar hajoji da cinikayyar makamashi. Tabbatar da tsaron yankin ya dace da moriyar bangarori daban daban na kasa da kasa. Ya kamata bangarori da abin ya shafa su dakatar da aikin soja nan da nan, da magance tsananta yanayin, da kawo illa ga sassan duniya a sakamakon yakin baki daya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post