ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masanan Afirka: Shirin Shekaru Biyar-biyar Na Kasar Sin Karo Na 15 Ya Ba Da Sabbin Damammaki Na Ci Gaba Ga Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Afirka

Shirin raya ci gaban kasa na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 da aka amince da shi a kwanan nan, ya samar da damammakin da kasashen Afirka za su iya amfani da su yayin da suke bin hanyoyinsu na samun ci gaba, kamar yadda manazarta suka bayyana a wani taron kara wa juna sani da aka gudanar a Kampala jiya Talata.

Taron, wanda aka gudanar bisa taken “Dabarun daidaita sahu don samun wadata: Zurfafa alakar da ke tsakanin Sin da Uganda a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 15,” ya samu halartar masu bincike, masana ilimi da kuma jami’an gwamnati. Cibiyar kwararrun masu nazari da ke sa-ido kan ci gaba, watau DWC da ke Uganda ce ta shirya taron.

Wani mai bincike na cibiyar DWC Arthur Atuha, ya bayyana cewa kasashe kamar Uganda za su iya cin gajiyar zurfafan fasahohin kimiyya da kirkire-kirkire na kasar Sin wajen sarrafa kayayyaki cikin hanzari domin kaiwa kasuwar kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kazalika, shi ma wani mai bincike a cibiyar binciken kimiyyar dan Adam ta Afirka ta Kudu Vuyo Mjimba, ya bayyana cewa shirin na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 ya nuna muhimmancin yadda kasashen Afirka za su ci gaba da dagewa wajen ba da fifiko ga ci gaban kansu, maimakon dogaro da tsare-tsaren wasu daga waje.

Har ila yau a nasa bangaren, wani jami’in bincike a cibiyar DWC Joshua Kingdom, ya bayyana cewa kasar Sin ta riga ta aza harsashi a yankin Afirka domin zurfafa cudanyar kasuwanci a yayin da take habaka zamanantarwa da kuma samun ci gaba mai inganci a matakin koli. Ya kara da cewa, a karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, watau BRI a takaice, kasar Sin ta ba da goyon baya ga gina muhimman kayayyakin more rayuwa na makamashi da sufuri, wadanda za su iya taimaka wa kasashen Afirka wajen yin amfani da damammakin da suka samu.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Sannan, Mai fashin baki a fannin tattalin arziki dan asalin kasar Guinea-Bissau Afonso Gomes ya bayyana cewa, manufar da kasar Sin ta sanar ta yafe harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 da ake shigarwa kasar Sin, za ta haifar da wani sabon mafari na yaukaka alakar Sin da kasashen nahiyar Afirka, kuma hakan zai kara karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Mr. Afonso Gomes ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawar baya bayan nan da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua.

Gomes ya ce, manufofin kasar Sin sun dace da aniyar kasar ta goyon bayan cudanyar mabambantan sassa, da zurfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka. Ya ce hakan zai bude sabbin damammaki ga kasashen nahiyar Afirka na fitar da karin hajoji da aka karawa inganci, da samar da guraben ayyukan yi a gida da fadada kudaden shigarsu. Kazalika, manufar za ta taimakawa kasashen Afirka da damar rage fatara, da karfafa ikon nahiyar na cimma dogaro da kai ta fuskar tattalin arziki.

Mista Gomes ya kara da cewa kasar Guinea-Bissau, wadda akasarin kayayyakin da take fitarwa na albarkatun gona ne, irinsu gyadar yazawa ko “cashew nuts”, na iya amfani da wannan zarafi wajen fadada, da ingiza sarrafa kayayyaki a cikin gida.

A mataki na shiyya kuwa, Gomes ya yi kira da a karfafa, da tsara salon tattaunawa a hukumance, tsakanin kasashe membobin kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka ko ECOWAS da bangaren Sin, ta yadda hakan zai taimaka wajen daidaita mizanin ingancin hajoji da bunkasa cinikayya. (Saminu Alhassan, Abdulrazaq Yahuz Jere)

 

 

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Takarar Tinubu Da Shettima Babbar Nasarar APC Ce – Buni

Harin Bam: Gwamnan Yobe Ya Bayar Da Tallafin ₦10m, Ya Jajantawa Al'ummar Borno 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.