ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masanan Afirka: Shirin Shekaru Biyar-biyar Na Kasar Sin Karo Na 15 Ya Ba Da Sabbin Damammaki Na Ci Gaba Ga Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Afirka

Shirin raya ci gaban kasa na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 da aka amince da shi a kwanan nan, ya samar da damammakin da kasashen Afirka za su iya amfani da su yayin da suke bin hanyoyinsu na samun ci gaba, kamar yadda manazarta suka bayyana a wani taron kara wa juna sani da aka gudanar a Kampala jiya Talata.

Taron, wanda aka gudanar bisa taken “Dabarun daidaita sahu don samun wadata: Zurfafa alakar da ke tsakanin Sin da Uganda a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 15,” ya samu halartar masu bincike, masana ilimi da kuma jami’an gwamnati. Cibiyar kwararrun masu nazari da ke sa-ido kan ci gaba, watau DWC da ke Uganda ce ta shirya taron.

Wani mai bincike na cibiyar DWC Arthur Atuha, ya bayyana cewa kasashe kamar Uganda za su iya cin gajiyar zurfafan fasahohin kimiyya da kirkire-kirkire na kasar Sin wajen sarrafa kayayyaki cikin hanzari domin kaiwa kasuwar kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kazalika, shi ma wani mai bincike a cibiyar binciken kimiyyar dan Adam ta Afirka ta Kudu Vuyo Mjimba, ya bayyana cewa shirin na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 ya nuna muhimmancin yadda kasashen Afirka za su ci gaba da dagewa wajen ba da fifiko ga ci gaban kansu, maimakon dogaro da tsare-tsaren wasu daga waje.

Har ila yau a nasa bangaren, wani jami’in bincike a cibiyar DWC Joshua Kingdom, ya bayyana cewa kasar Sin ta riga ta aza harsashi a yankin Afirka domin zurfafa cudanyar kasuwanci a yayin da take habaka zamanantarwa da kuma samun ci gaba mai inganci a matakin koli. Ya kara da cewa, a karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, watau BRI a takaice, kasar Sin ta ba da goyon baya ga gina muhimman kayayyakin more rayuwa na makamashi da sufuri, wadanda za su iya taimaka wa kasashen Afirka wajen yin amfani da damammakin da suka samu.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sannan, Mai fashin baki a fannin tattalin arziki dan asalin kasar Guinea-Bissau Afonso Gomes ya bayyana cewa, manufar da kasar Sin ta sanar ta yafe harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 da ake shigarwa kasar Sin, za ta haifar da wani sabon mafari na yaukaka alakar Sin da kasashen nahiyar Afirka, kuma hakan zai kara karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Mr. Afonso Gomes ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawar baya bayan nan da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua.

Gomes ya ce, manufofin kasar Sin sun dace da aniyar kasar ta goyon bayan cudanyar mabambantan sassa, da zurfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka. Ya ce hakan zai bude sabbin damammaki ga kasashen nahiyar Afirka na fitar da karin hajoji da aka karawa inganci, da samar da guraben ayyukan yi a gida da fadada kudaden shigarsu. Kazalika, manufar za ta taimakawa kasashen Afirka da damar rage fatara, da karfafa ikon nahiyar na cimma dogaro da kai ta fuskar tattalin arziki.

Mista Gomes ya kara da cewa kasar Guinea-Bissau, wadda akasarin kayayyakin da take fitarwa na albarkatun gona ne, irinsu gyadar yazawa ko “cashew nuts”, na iya amfani da wannan zarafi wajen fadada, da ingiza sarrafa kayayyaki a cikin gida.

A mataki na shiyya kuwa, Gomes ya yi kira da a karfafa, da tsara salon tattaunawa a hukumance, tsakanin kasashe membobin kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka ko ECOWAS da bangaren Sin, ta yadda hakan zai taimaka wajen daidaita mizanin ingancin hajoji da bunkasa cinikayya. (Saminu Alhassan, Abdulrazaq Yahuz Jere)

 

 

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Takarar Tinubu Da Shettima Babbar Nasarar APC Ce – Buni

Harin Bam: Gwamnan Yobe Ya Bayar Da Tallafin ₦10m, Ya Jajantawa Al'ummar Borno 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.