ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masanan Afirka: Shirin Shekaru Biyar-biyar Na Kasar Sin Karo Na 15 Ya Ba Da Sabbin Damammaki Na Ci Gaba Ga Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Afirka

Shirin raya ci gaban kasa na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 da aka amince da shi a kwanan nan, ya samar da damammakin da kasashen Afirka za su iya amfani da su yayin da suke bin hanyoyinsu na samun ci gaba, kamar yadda manazarta suka bayyana a wani taron kara wa juna sani da aka gudanar a Kampala jiya Talata.

Taron, wanda aka gudanar bisa taken “Dabarun daidaita sahu don samun wadata: Zurfafa alakar da ke tsakanin Sin da Uganda a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 15,” ya samu halartar masu bincike, masana ilimi da kuma jami’an gwamnati. Cibiyar kwararrun masu nazari da ke sa-ido kan ci gaba, watau DWC da ke Uganda ce ta shirya taron.

Wani mai bincike na cibiyar DWC Arthur Atuha, ya bayyana cewa kasashe kamar Uganda za su iya cin gajiyar zurfafan fasahohin kimiyya da kirkire-kirkire na kasar Sin wajen sarrafa kayayyaki cikin hanzari domin kaiwa kasuwar kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Kazalika, shi ma wani mai bincike a cibiyar binciken kimiyyar dan Adam ta Afirka ta Kudu Vuyo Mjimba, ya bayyana cewa shirin na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 ya nuna muhimmancin yadda kasashen Afirka za su ci gaba da dagewa wajen ba da fifiko ga ci gaban kansu, maimakon dogaro da tsare-tsaren wasu daga waje.

Har ila yau a nasa bangaren, wani jami’in bincike a cibiyar DWC Joshua Kingdom, ya bayyana cewa kasar Sin ta riga ta aza harsashi a yankin Afirka domin zurfafa cudanyar kasuwanci a yayin da take habaka zamanantarwa da kuma samun ci gaba mai inganci a matakin koli. Ya kara da cewa, a karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, watau BRI a takaice, kasar Sin ta ba da goyon baya ga gina muhimman kayayyakin more rayuwa na makamashi da sufuri, wadanda za su iya taimaka wa kasashen Afirka wajen yin amfani da damammakin da suka samu.

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Sannan, Mai fashin baki a fannin tattalin arziki dan asalin kasar Guinea-Bissau Afonso Gomes ya bayyana cewa, manufar da kasar Sin ta sanar ta yafe harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 da ake shigarwa kasar Sin, za ta haifar da wani sabon mafari na yaukaka alakar Sin da kasashen nahiyar Afirka, kuma hakan zai kara karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Mr. Afonso Gomes ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawar baya bayan nan da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua.

Gomes ya ce, manufofin kasar Sin sun dace da aniyar kasar ta goyon bayan cudanyar mabambantan sassa, da zurfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka. Ya ce hakan zai bude sabbin damammaki ga kasashen nahiyar Afirka na fitar da karin hajoji da aka karawa inganci, da samar da guraben ayyukan yi a gida da fadada kudaden shigarsu. Kazalika, manufar za ta taimakawa kasashen Afirka da damar rage fatara, da karfafa ikon nahiyar na cimma dogaro da kai ta fuskar tattalin arziki.

Mista Gomes ya kara da cewa kasar Guinea-Bissau, wadda akasarin kayayyakin da take fitarwa na albarkatun gona ne, irinsu gyadar yazawa ko “cashew nuts”, na iya amfani da wannan zarafi wajen fadada, da ingiza sarrafa kayayyaki a cikin gida.

A mataki na shiyya kuwa, Gomes ya yi kira da a karfafa, da tsara salon tattaunawa a hukumance, tsakanin kasashe membobin kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka ko ECOWAS da bangaren Sin, ta yadda hakan zai taimaka wajen daidaita mizanin ingancin hajoji da bunkasa cinikayya. (Saminu Alhassan, Abdulrazaq Yahuz Jere)

 

 

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

MASU ALAKA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
Daga Birnin Sin

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Next Post
Takarar Tinubu Da Shettima Babbar Nasarar APC Ce – Buni

Harin Bam: Gwamnan Yobe Ya Bayar Da Tallafin ₦10m, Ya Jajantawa Al'ummar Borno 

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.