ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Zuba Jari Na Waje Suna Da Kyakkyawan Fata Game Da Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Bayan da hukumar gwamnatin kasar Sin ta fitar da alkaluman tattalin arziki na watanni biyu da suka gabata a jiya Litinin, kafofoin watsa labarai na kasashen waje, kamar Jaridar Wall Street, sun jinjinawa gagarumin ci gaba mai ban mamaki da Sin ta samu a fannonin kashe kudi, da raya masana’antu da dai sauransu.

To ko me ya sa suka bayyana hakan? Akwai dalilai guda biyu. Na farko shi ne Sin ta bunkasa tattalin arziki cikin kwanciyar hankali. Inda a watanni biyu da suka gabata, saurin karuwar yawancin manyan alamomin tattalin arziki na Sin ya samu ci gaba, idan aka kwantanta da shekarar bara baki daya.

  • Sin Na Adawa Da Haramta Amfani Da DeepSeek Da Gwamnatin Amurka Ta Yi
  • Trump Zai Tattauna Da Putin Kan Kawo Ƙarshen Yaƙin Ukraine

Alal misali, yawan karuwar masana’antu masu babban ma’auni na kasar ya kai kashi 5.9 bisa dari kan na makamancin lokaci na bara, inda saurin karuwarsa ya kai kashi 0.1 bisa dari kan na shekarar bara baki daya, kuma saurin karuwar zuba jari kan kadarori ya karu da kashi 0.9 bisa dari, idan aka kwantanta da na shekarar bara baki daya. Bisa wadannan alamomi, ana iya ganin cewa tattalin arzikin Sin ya kiyaye yanayin farfadowa, tun daga kwata ta hudu ta shekarar bara, kuma ya kasance cikin yanayi mai nagarta.

ADVERTISEMENT

Na biyu shi ne, tattalin arzikin Sin ya ci gaba da karuwa a fannin fasahohin zamani. A cikin watanni biyu da suka gabata, saurin karuwar darajar masana’antun kere-keren fasahohin zamani na kasar, ya karu da kashi 0.2 bisa dari kan na makamancin lokaci na bara, inda saurin karuwar zuba jari na masana’antun fasahohin zamani ya fi samun saurin karuwar zuba jari baki daya, wanda hakan ya nuna cewa, sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko na ci gaba da bunkasuwa cikin kwanciyar hankali.

Bisa irin wadannan nasarori da Sin ta cimma, a cikin wani dan lokaci, kafofin watsa labarai na waje sun yaba da karsashin tattalin arzikin kasar Sin sosai.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Jaridar Financial Times ta Burtaniya ta bayyana cewa, masu zuba jari na kasashen waje suna kara “gano kasar Sin”, kuma sun yi imanin cewa, kasar Sin za ta iya samar da “kirkire-kirkire da damammaki” masu yawa a wasu fannoni. (Safiyah Ma)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Dakatar Da Gwamna Fubara: Tinubu Ya Naɗa Tsohon Hafsan Sojin Ruwa A Matsayin Mai Kula Da Jihar Ribas

Dakatar Da Gwamna Fubara: Tinubu Ya Naɗa Tsohon Hafsan Sojin Ruwa A Matsayin Mai Kula Da Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.