Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, kasar ta nuna matukar rashin amincewarta ga jakadan kasar Philippines bisa tsokanar fada da kuma kai hari kan jami’an tsaron tekun kasar Sin (CCG) a yankin teku na Ren’ai Jiao, inda ta kara da cewa, kasar Sin ta yi tsayuwar daka wajen kiyaye ikon mallakar yankinta da moriyarta ta teku.
Mai magana da yawun ma’aikatar, Lin Jian ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai na yau da kullum yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da lamarin, inda ya bukaci Philippines da ta daina tayar da husuma da wuce-gona-da-iri.
A cewar kakakin, a ranar 20 ga watan Yuli, wasu kananan jiragen ruwa guda biyu da suka fito daga wani babban jirgin ruwa na Philippines da ya ja tunga, sun tunkari wani jirgin sintiri na CCG cikin wani yanayi mai hadari inda suka gwabza masa karo da karfi, kana bangaren na Philippines ya kai farmaki kan jami’an tsaron kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














