Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kabiru Gaya, ya amince ya koma jam’iyyar APC.
Rahotanni sun bayyana cewar Gaya ya yanke wannan shawara ne bayan wata ganawar sirri da ya yi da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Nentawe Yilwatda, a gidansa da ke birnin Tarayya, Abuja a daren ranar Litinin.
Ganawar ta ɗauki kusan mintuna 45.
Wata majiya ta tabbatar da cewa Kabiru Gaya ya amince zai koma jam’iyyar APC.
Matakin na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da rahotanni suka bayyana cewa Gaya bai samu tikitin takarar Sanatan Kano ta Kudu na jam’iyyar NDC ba domin shiga zaɓen shekarar 2027.
Kabiru Gaya ya fice daga APC a ranar 5 ga watan Afrilu.
Daga nan ya koma jam’iyyar ADC kafin daga bisani ya koma NDC tare da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.
Gaya ya taɓa yin Gwamnan Jihar Kano tsakanin 1992 zuwa 1993 a lokacin Jamhuriya ta Uku.
Daga bisani kuma ya wakilci yankin Kano ta Kudu a Majalisar Dattawa daga 2015 zuwa 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar APC.
A zaɓen shekarar 2023, Gaya ya sha kaye a hannun Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila na jam’iyyar NNPP.
Shi ma Kawu ya fice daga NNPP tare da komawa jam’iyyar APC.














