ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

by Zubairu M Lawal
4 hours ago

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce gwamnatin jihar na sa ran samun aƙalla Dalar Amurka miliyan 10 daga harkar haƙowa da sarrafa ma’adinin lithium kafin ƙarshen wannan shekara.

Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin ƙaddamar da titin Agwada zuwa Udege mai tsawon kilomita 12.4 da ke Ƙaramar Hukumar Kokona, bayan dawowarsa daga wata tafiya zuwa Amurka domin nemo masu zuba jari.

Gwamna Sule ya ce za a yi amfani da kuɗaɗen wajen gudanar da ayyukan ci gaba a jihar, musamman a yankin Endo da ke Kokona, inda aka gina ɗaya daga cikin manyan masana’antun sarrafa lithium a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya ce gwamnatin jihar ta cimma yarjejeniya da kamfanin Ganfeng Mining Company Limited, wanda jihar za ta karbi Dalar Amurka miliyan 15 cikin shekaru 10.

Haka kuma, al’ummar Endo za su samu Dalar Amurka 500,000 domin ayyukan ci gaban yankinsu.

LABARAI MASU NASABA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

Gwamnan ya ƙara da cewa kuɗaɗen shiga daga ma’adinai a jihar sun zarce Naira biliyan ɗaya a kowane wata, sakamakon zuba jarin da ya kai Dalar Amurka miliyan 850 a masana’antar sarrafa lithium.

A cewarsa, ƙarin masu zuba jari na nuna amincewa da damar da jihar ke da ita a ɓangaren ma’adinai, lamarin da ya sa Nasarawa ta zama ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin haƙar da sarrafa lithium a Nijeriya.

Sule ya kuma bayyana cewa ziyararsa zuwa Amurka ta jawo hankalin masu zuba jari da jami’an gwamnatin ƙasar, waɗanda suka nuna sha’awar saka hannun jari a lithium da sauran ma’adinan da ke jihar.

Ya ce Ministan Ma’adinai, Dokta Dele Alake, zai ci gaba da tattaunawa da masu zuba jari a Amurka, yayin da shi kuma zai kai ziyara ƙasar China domin neman ƙarin masu zuba jari zuwa jihar.

Gwamnan ya ce ƙarin kuɗaɗen shiga daga ma’adinai da kuma ƙarin rabon kuɗaɗen gwamnatin tarayya sun taimaka wajen yin ayyukan raya ƙasa a jihar.

Ya bayyana cewa ana ci gaba da gina hanyoyi da dama, ciki har da titunan Nasarawa Eggon–Mada Station da Nasarawa–Ara, domin inganta sufuri da tallafa wa noma, haƙar ma’adinai da kasuwanci.

A yayin taron, Gwamna Sule ya ƙaddamar da titin Agwada zuwa Udege mai tsawon kilomita 12.4 da aka gina kan kuɗivNaira biliyan 4.401.

Titin ya haɗa Ƙaramar Hukumar Kokona da Ƙaramar Hukumar Nasarawa, kuma ana sa ran zai rage lokacin tafiya tare da sauƙaƙa jigilar amfanin gona da ma’adinai.

A ƙarshe, gwamnan ya yaba wa kamfanin da ya gina titin saboda kammala aikin ba tare da neman ƙarin kuɗin kwangila ba, yana mai cewa gwamnatinsa ba ta amincewa da ƙarin kudin kwangila bayan an ƙulla yarjejeniya.

Zubairu M Lawal
+ postsBio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tinubu Ya Ƙaddamar Da Gadar Ƙasa Da Tituna A Akwanga
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kamfanin Haƙar Ma’adanai Saboda Rikicin Shari’a
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnati Ta Jibge Jami’an Tsaro Domin Gudanar da Zaɓen Fidda Gwanin APC A Nasarawa

MASU ALAKA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
nema
Manyan Labarai

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026
Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.