Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce gwamnatin jihar na sa ran samun aƙalla Dalar Amurka miliyan 10 daga harkar haƙowa da sarrafa ma’adinin lithium kafin ƙarshen wannan shekara.
Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin ƙaddamar da titin Agwada zuwa Udege mai tsawon kilomita 12.4 da ke Ƙaramar Hukumar Kokona, bayan dawowarsa daga wata tafiya zuwa Amurka domin nemo masu zuba jari.
Gwamna Sule ya ce za a yi amfani da kuɗaɗen wajen gudanar da ayyukan ci gaba a jihar, musamman a yankin Endo da ke Kokona, inda aka gina ɗaya daga cikin manyan masana’antun sarrafa lithium a Nijeriya.
Ya ce gwamnatin jihar ta cimma yarjejeniya da kamfanin Ganfeng Mining Company Limited, wanda jihar za ta karbi Dalar Amurka miliyan 15 cikin shekaru 10.
Haka kuma, al’ummar Endo za su samu Dalar Amurka 500,000 domin ayyukan ci gaban yankinsu.
Gwamnan ya ƙara da cewa kuɗaɗen shiga daga ma’adinai a jihar sun zarce Naira biliyan ɗaya a kowane wata, sakamakon zuba jarin da ya kai Dalar Amurka miliyan 850 a masana’antar sarrafa lithium.
A cewarsa, ƙarin masu zuba jari na nuna amincewa da damar da jihar ke da ita a ɓangaren ma’adinai, lamarin da ya sa Nasarawa ta zama ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin haƙar da sarrafa lithium a Nijeriya.
Sule ya kuma bayyana cewa ziyararsa zuwa Amurka ta jawo hankalin masu zuba jari da jami’an gwamnatin ƙasar, waɗanda suka nuna sha’awar saka hannun jari a lithium da sauran ma’adinan da ke jihar.
Ya ce Ministan Ma’adinai, Dokta Dele Alake, zai ci gaba da tattaunawa da masu zuba jari a Amurka, yayin da shi kuma zai kai ziyara ƙasar China domin neman ƙarin masu zuba jari zuwa jihar.
Gwamnan ya ce ƙarin kuɗaɗen shiga daga ma’adinai da kuma ƙarin rabon kuɗaɗen gwamnatin tarayya sun taimaka wajen yin ayyukan raya ƙasa a jihar.
Ya bayyana cewa ana ci gaba da gina hanyoyi da dama, ciki har da titunan Nasarawa Eggon–Mada Station da Nasarawa–Ara, domin inganta sufuri da tallafa wa noma, haƙar ma’adinai da kasuwanci.
A yayin taron, Gwamna Sule ya ƙaddamar da titin Agwada zuwa Udege mai tsawon kilomita 12.4 da aka gina kan kuɗivNaira biliyan 4.401.
Titin ya haɗa Ƙaramar Hukumar Kokona da Ƙaramar Hukumar Nasarawa, kuma ana sa ran zai rage lokacin tafiya tare da sauƙaƙa jigilar amfanin gona da ma’adinai.
A ƙarshe, gwamnan ya yaba wa kamfanin da ya gina titin saboda kammala aikin ba tare da neman ƙarin kuɗin kwangila ba, yana mai cewa gwamnatinsa ba ta amincewa da ƙarin kudin kwangila bayan an ƙulla yarjejeniya.














