Rundunar ‘Yansandan Jihar Bauchi ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da satar shanu, tare da ƙwato bijimai uku da ake kyautata zaton na sata ne, waɗanda darajarsu ta kai Naira miliyan 1.73.
An kama su ne a Ƙaramar Hukumar Alkaleri ta jihar.
Waɗanda ake zargin su ne Umaru Adamu mai shekara 40, wanda aka fi sani da Balawo, da Haruna Usman mai shekara 30, wanda aka fi sani da Dotti.
Dukkansu sun fito ne daga ƙauyen Dawo da ke Ƙaramar Hukumar Kwami a Jihar Gombe.
An kama su ne a ranar 19 ga watan Yuli, 2026.
Kakakin Rundunar ‘Yansandan Jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya ce jami’an ‘yansanda na Sashen Alkaleri ne suka kama mutanen da misalin ƙarfe 2 na rana, bayan samu. sahihan bayanan sirri.
‘Yansandan sun ce bijiman guda ukun da aka samu a hannun waɗanda ake zargin ana kyautata zaton an sato su ne.
Bincike ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun karɓi shanun ne daga wasu mutane biyu da ke gudun hijira.
Rundunar ta ce ana zargin mutanen da suka tsere sun daɗe suna aikata satar shanu a yankunan da ke iyakar jihohin Bauchi da Gombe.
Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci jami’ansa su ƙara ƙaimi wajen gano tare da cafke sauran waɗanda suka tsere.
A halin yanzu, mutanen biyun na hannun ‘yansanda yayin da ake ci gaba da bincike.
Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimakawa wajen yaƙi da satar shanu da sauran laifuka a jihar.














